• English
  • Business News
Wednesday, July 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Da Afirka Za Su Ci Gaba Da Aiwatar Da Tsare-tsaren Ayyukan Hadin Gwiwa 10 

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Da Afirka Za Su Ci Gaba Da Aiwatar Da Tsare-tsaren Ayyukan Hadin Gwiwa 10 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya bayyana a jiya Juma’a cewa, kasar Sin a shirye take ta yi aiki tare da kasashen Afirka wajen samar da sakamako masu inganci daga tsaren-tsaren ayyukan hadin gwiwa 10 da aka gabatar a taron kolin dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka (FOCAC) da aka gudanar a birnin Beijing a shekarar da ta gabata, tare da tabbatar da cewa, bangarorin biyu sun samu ci gaba kan hanyar zamanantarwa cikin sauri, da kwanciyar hankali.

Wang ya bayyana hakan ne a wata hirar da ya yi da kafafen yada labarai na kasar Sin bayan ziyarar da ya kai kasashen Namibia, Jamhuriyar Kongo, Chadi da Najeriya.

  • Kasuwar ‘Yan Wasa: Omar Marmoush Na Dab Da Komawa Manchester City
  • Za Mu Tabbatar Da Samun Kyakkyawar Alaka Da Gwamnati Don Ci Gaban Kasuwar Kofar Ruwa – ‘Yanleman

Wang ya kara da cewa, shugaban Jamhuriyar Kongo Denis Sassou Nguesso da wasu shugabannin kasashen Afirka sun bayyana cewa, tsare-tsaren ayyukan hadin gwiwa guda 10, sun shafi dukkan fannoni na hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka, da tinkarar kalubalen da Afirka ke fuskanta, da daidaita bukatun Afirka, kuma za su ba da goyon baya mai yawa ga ci gaba da farfadowar nahiyar ta Afirka.

Kazalika, kasar Sin a shirye take ta yi aiki tare da kasashen Afirka wajen sa kaimi ga gudanar da harkokin daidaita sauyin yanayi a duniya, da kiyaye ka’idar “ana tare a zahiri amma an sha bamban a daukar alhaki”, kana ta bukaci kasashe masu ci gaba da su amince da nauyin da ke wuyansu na tarihi, da kuma sauke nauyin da aka rataya a wuyansu, da ba da tallafi na kudi, fasaha, da kara sanin makamar aiki ga kasashe masu tasowa, musamman ma kasashen Afirka.

A hadin gwiwa a fannin aikin gona kuwa, ministan harkokin wajen kasar Sin ya bayyana wasu muhimman fannoni guda biyar da kasar Sin za ta mai da hankali a kai, wadanda suka hada da samar da abinci, da rage fatara, da kara sanin makamar aiki, da saukaka harkokin kasuwanci, da sada zumunta, domin gaggauta aiwatar da sakamakon taron kolin FOCAC na Beijing a fannin aikin gona.

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

Da yake karin haske game da yadda kasashe masu tasowa ke samun ci gaba duk da sauye-sauyen da duniya ke fuskanta, Wang ya ce, Sin da Afirka su ne ginshikann ci gaba da farfado da kasashe masu tasowa na duniya, kuma suna da ra’ayin gina tsarin tafiyar da harkokin duniya mai adalci da daidaici.

Wang ya ci gada da cewa, a matsayinta na muhimmiyar aminiya kuma abokiyar huldar Afirka, kasar Sin za ta ci gaba da ba da goyon baya ga kasashen Afirka ba tare da kakkautawa ba, wajen gyara zaluncin da aka yi musu a tarihi, da yin kakkausar suka ga duk wani tsoma bakin waje a harkokin cikin gidan Afirka, tare da ba da shawarar samar da shirye-shirye na musamman don tinkarar matsalolin Afirka wajen yin kwaskwarima ga kwamitin sulhu na MDD. (Mohammed Yahaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasuwar ‘Yan Wasa: Omar Marmoush Na Dab Da Komawa Manchester City

Next Post

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ta Kawo Moriya Ga Bunkasar Masar

Related

Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

9 hours ago
Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa
Daga Birnin Sin

Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

17 hours ago
Babatun Lai Ching-Te Ba Zai Taba Girgiza Kasancewar Sin Day Tak A Duniya Ba
Daga Birnin Sin

Babatun Lai Ching-Te Ba Zai Taba Girgiza Kasancewar Sin Day Tak A Duniya Ba

18 hours ago
Kamfanin Sin Ya Cimma Nasarar Shimfida Layin Dogo Na Farko Dakon Kaya Mafiya Nauyi A Hamadar Afirka
Daga Birnin Sin

Kamfanin Sin Ya Cimma Nasarar Shimfida Layin Dogo Na Farko Dakon Kaya Mafiya Nauyi A Hamadar Afirka

19 hours ago
An Bude Taron Layin Dogo Mai Saurin Gudu Na Duniya Karo Na 12 A Beijing
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Layin Dogo Mai Saurin Gudu Na Duniya Karo Na 12 A Beijing

20 hours ago
Sin Za Ta Yi Aiki Da MDD Don Samar Da Jagorancin Duniya Mai Cike Da Adalci Da Daidaito
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Yi Aiki Da MDD Don Samar Da Jagorancin Duniya Mai Cike Da Adalci Da Daidaito

21 hours ago
Next Post
Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ta Kawo Moriya Ga Bunkasar Masar

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ta Kawo Moriya Ga Bunkasar Masar

LABARAI MASU NASABA

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

July 9, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Babu Wanda Ya Buƙaci Atiku Ka Da Ya Yi Takara A 2027 – ADC

July 9, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza

July 9, 2025
Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

July 9, 2025
Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

July 9, 2025
Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

July 9, 2025
Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

July 9, 2025
Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

July 9, 2025
Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

July 8, 2025
Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

July 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.