ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Da Afirka Za Su Ci Gaba Da Aiwatar Da Tsare-tsaren Ayyukan Hadin Gwiwa 10 

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Sin

Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya bayyana a jiya Juma’a cewa, kasar Sin a shirye take ta yi aiki tare da kasashen Afirka wajen samar da sakamako masu inganci daga tsaren-tsaren ayyukan hadin gwiwa 10 da aka gabatar a taron kolin dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka (FOCAC) da aka gudanar a birnin Beijing a shekarar da ta gabata, tare da tabbatar da cewa, bangarorin biyu sun samu ci gaba kan hanyar zamanantarwa cikin sauri, da kwanciyar hankali.

Wang ya bayyana hakan ne a wata hirar da ya yi da kafafen yada labarai na kasar Sin bayan ziyarar da ya kai kasashen Namibia, Jamhuriyar Kongo, Chadi da Najeriya.

  • Kasuwar ‘Yan Wasa: Omar Marmoush Na Dab Da Komawa Manchester City
  • Za Mu Tabbatar Da Samun Kyakkyawar Alaka Da Gwamnati Don Ci Gaban Kasuwar Kofar Ruwa – ‘Yanleman

Wang ya kara da cewa, shugaban Jamhuriyar Kongo Denis Sassou Nguesso da wasu shugabannin kasashen Afirka sun bayyana cewa, tsare-tsaren ayyukan hadin gwiwa guda 10, sun shafi dukkan fannoni na hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka, da tinkarar kalubalen da Afirka ke fuskanta, da daidaita bukatun Afirka, kuma za su ba da goyon baya mai yawa ga ci gaba da farfadowar nahiyar ta Afirka.

ADVERTISEMENT

Kazalika, kasar Sin a shirye take ta yi aiki tare da kasashen Afirka wajen sa kaimi ga gudanar da harkokin daidaita sauyin yanayi a duniya, da kiyaye ka’idar “ana tare a zahiri amma an sha bamban a daukar alhaki”, kana ta bukaci kasashe masu ci gaba da su amince da nauyin da ke wuyansu na tarihi, da kuma sauke nauyin da aka rataya a wuyansu, da ba da tallafi na kudi, fasaha, da kara sanin makamar aiki ga kasashe masu tasowa, musamman ma kasashen Afirka.

A hadin gwiwa a fannin aikin gona kuwa, ministan harkokin wajen kasar Sin ya bayyana wasu muhimman fannoni guda biyar da kasar Sin za ta mai da hankali a kai, wadanda suka hada da samar da abinci, da rage fatara, da kara sanin makamar aiki, da saukaka harkokin kasuwanci, da sada zumunta, domin gaggauta aiwatar da sakamakon taron kolin FOCAC na Beijing a fannin aikin gona.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Da yake karin haske game da yadda kasashe masu tasowa ke samun ci gaba duk da sauye-sauyen da duniya ke fuskanta, Wang ya ce, Sin da Afirka su ne ginshikann ci gaba da farfado da kasashe masu tasowa na duniya, kuma suna da ra’ayin gina tsarin tafiyar da harkokin duniya mai adalci da daidaici.

Wang ya ci gada da cewa, a matsayinta na muhimmiyar aminiya kuma abokiyar huldar Afirka, kasar Sin za ta ci gaba da ba da goyon baya ga kasashen Afirka ba tare da kakkautawa ba, wajen gyara zaluncin da aka yi musu a tarihi, da yin kakkausar suka ga duk wani tsoma bakin waje a harkokin cikin gidan Afirka, tare da ba da shawarar samar da shirye-shirye na musamman don tinkarar matsalolin Afirka wajen yin kwaskwarima ga kwamitin sulhu na MDD. (Mohammed Yahaya)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ta Kawo Moriya Ga Bunkasar Masar

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ta Kawo Moriya Ga Bunkasar Masar

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.