ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Da Afirka Za Su Ci Gaba Da Aiwatar Da Tsare-tsaren Ayyukan Hadin Gwiwa 10 

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Sin

Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya bayyana a jiya Juma’a cewa, kasar Sin a shirye take ta yi aiki tare da kasashen Afirka wajen samar da sakamako masu inganci daga tsaren-tsaren ayyukan hadin gwiwa 10 da aka gabatar a taron kolin dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka (FOCAC) da aka gudanar a birnin Beijing a shekarar da ta gabata, tare da tabbatar da cewa, bangarorin biyu sun samu ci gaba kan hanyar zamanantarwa cikin sauri, da kwanciyar hankali.

Wang ya bayyana hakan ne a wata hirar da ya yi da kafafen yada labarai na kasar Sin bayan ziyarar da ya kai kasashen Namibia, Jamhuriyar Kongo, Chadi da Najeriya.

  • Kasuwar ‘Yan Wasa: Omar Marmoush Na Dab Da Komawa Manchester City
  • Za Mu Tabbatar Da Samun Kyakkyawar Alaka Da Gwamnati Don Ci Gaban Kasuwar Kofar Ruwa – ‘Yanleman

Wang ya kara da cewa, shugaban Jamhuriyar Kongo Denis Sassou Nguesso da wasu shugabannin kasashen Afirka sun bayyana cewa, tsare-tsaren ayyukan hadin gwiwa guda 10, sun shafi dukkan fannoni na hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka, da tinkarar kalubalen da Afirka ke fuskanta, da daidaita bukatun Afirka, kuma za su ba da goyon baya mai yawa ga ci gaba da farfadowar nahiyar ta Afirka.

ADVERTISEMENT

Kazalika, kasar Sin a shirye take ta yi aiki tare da kasashen Afirka wajen sa kaimi ga gudanar da harkokin daidaita sauyin yanayi a duniya, da kiyaye ka’idar “ana tare a zahiri amma an sha bamban a daukar alhaki”, kana ta bukaci kasashe masu ci gaba da su amince da nauyin da ke wuyansu na tarihi, da kuma sauke nauyin da aka rataya a wuyansu, da ba da tallafi na kudi, fasaha, da kara sanin makamar aiki ga kasashe masu tasowa, musamman ma kasashen Afirka.

A hadin gwiwa a fannin aikin gona kuwa, ministan harkokin wajen kasar Sin ya bayyana wasu muhimman fannoni guda biyar da kasar Sin za ta mai da hankali a kai, wadanda suka hada da samar da abinci, da rage fatara, da kara sanin makamar aiki, da saukaka harkokin kasuwanci, da sada zumunta, domin gaggauta aiwatar da sakamakon taron kolin FOCAC na Beijing a fannin aikin gona.

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Da yake karin haske game da yadda kasashe masu tasowa ke samun ci gaba duk da sauye-sauyen da duniya ke fuskanta, Wang ya ce, Sin da Afirka su ne ginshikann ci gaba da farfado da kasashe masu tasowa na duniya, kuma suna da ra’ayin gina tsarin tafiyar da harkokin duniya mai adalci da daidaici.

Wang ya ci gada da cewa, a matsayinta na muhimmiyar aminiya kuma abokiyar huldar Afirka, kasar Sin za ta ci gaba da ba da goyon baya ga kasashen Afirka ba tare da kakkautawa ba, wajen gyara zaluncin da aka yi musu a tarihi, da yin kakkausar suka ga duk wani tsoma bakin waje a harkokin cikin gidan Afirka, tare da ba da shawarar samar da shirye-shirye na musamman don tinkarar matsalolin Afirka wajen yin kwaskwarima ga kwamitin sulhu na MDD. (Mohammed Yahaya)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • Sulaiman
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • Sulaiman
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

MASU ALAKA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
Daga Birnin Sin

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
Daga Birnin Sin

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Next Post
Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ta Kawo Moriya Ga Bunkasar Masar

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ta Kawo Moriya Ga Bunkasar Masar

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.