• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Da Amurka Za Su Iya Samar Da Alfanu Ga Duniya a Hadin Gwiwarsu

by CGTN Hausa and Sulaiman
9 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Da Amurka Za Su Iya Samar Da Alfanu Ga Duniya a Hadin Gwiwarsu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun daga tsakiyar wannan wata da muke ciki, Sin da Amurka su ke cudanya a bangarori daban-daban. Game da hakan, Sin ta bayyana cewa, kasashen biyu za su samu nagartattun ci gaba masu armashi tare da samar da alfanu ga al’ummun duniya, a mabambantan bangarori, illa dai suka yi hadin gwiwa. 

Manazarta na ganin cewa, ana fitar da sako mai yakini, duba da cewa bangarorin Sin da Amurka suna kara mu’ammala tsakaninsu, a daidai wannan lokacin da ake sauya gwamnati a kasar Amurka.

  • Yadda Sin Da Kasashen Afirka Ke Hadin Gwiwar Zamanantar Da Ayyukan Noma
  • Kasar Sin Ta Bukaci EU Ta Samar Da Ci Gaba Game Tattaunawar Da Suke Yi Kan Farashin Motoci Masu Amfani Da Lantarki Na Sin

A wata mai zuwa, Amurka za ta samu sabuwar gwamnati, kuma zababben shugaban kasar Donald Trump ya bayyana a kwanan baya cewa, za a iya warware kowacce matsala da ake fuskanta a duniya, idan Sin da Amurka suka hada kansu. Daga furucin nasa, za a iya fahimtar cewa, Amurka ta fahimci muhimmancin hadin kanta da kasar Sin, wanda mataki ne da zai amfana wajen rage rashin tabbaci a nan gaba, musamman ma a fannin huldar kasashen biyu. Hakika hanyar da ta fi dacewa, wadda sabuwar gwamnatin Amurka za ta iya bi, ita ce mutunta tsare-tsare da hanyoyin hadin gwiwa da bangarorin biyu suka riga suka tsara, da ma gabatar da karin sabbin hanyoyi da dabaru masu alaka da yunkurin kyautata huldarsu ta hadin kai.

Duk duniya sun kai ga matsaya daya cewa, kyautatuwar huldar Sin da Amurka mai dorewa ba al’ummar kasashen biyu kadai ta shafa ba, har ma da bayar da babbar ma’ana ga makomar Bil Adama ta bai daya. Duniya na fatan ganin bangarorin biyu za su kara tuntubar juna, da habaka hadin gwiwarsu, da warware matsaloli bisa iyakacin kokari a tsakaninsu, ta yadda za a sauke nauyin dake wuyan wadannan manyan kasashe guda 2, don karfafa hadin gwiwarsu da zai amfanawa al’ummar duniya, gami da samar da karin tabbaci da al’ummun kasa da kasa suke bukata. (Amina Xu)

 

Labarai Masu Nasaba

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

2027: ‘Yan Majalisan Adawa 18 Suka Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC

Next Post

Shugaban Kasa A 2027: Dan Takara Mai Nagarta Kawai Nijeriya Ke Bukata – Shekarau

Related

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana
Daga Birnin Sin

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

18 hours ago
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

19 hours ago
Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping
Daga Birnin Sin

Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

19 hours ago
Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

20 hours ago
Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

21 hours ago
Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira
Daga Birnin Sin

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

22 hours ago
Next Post
Shugaban Kasa A 2027: Dan Takara Mai Nagarta Kawai Nijeriya Ke Bukata – Shekarau

Shugaban Kasa A 2027: Dan Takara Mai Nagarta Kawai Nijeriya Ke Bukata – Shekarau

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

September 6, 2025
Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

September 6, 2025
Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

September 6, 2025
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

September 6, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

September 6, 2025
Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

September 6, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

September 6, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

September 6, 2025
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

September 6, 2025

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.