• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Da Angola Sun Daga Matsayin Dangantakarsu

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Da Angola Sun Daga Matsayin Dangantakarsu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yau Jumma’a, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya gana da takwaransa na Angola Joao Lourenco a nan birnin Beijing, inda shugabannin biyu suka sanar da daga matsayin dangantakarsu zuwa ta hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare.

Xi Jinping ya bayyana cewa, Sin abokiyar dogaro ce kuma sahihiyar abokiyar hulda ga kasashen Afrika wajen kare cikakken ‘yancinsu da inganta ci gabansu da farfadowarsu. Ya ce, Sin na goyon bayan kasashen Afrika da ma Tarayyar Afrika (AU), a kokarinsu na warware batutuwan da suka shafi Afrika bisa dabarun Afrika da kuma kare tsaro da zaman lafiya a nahiyar.

  • Tallafin Da Amurka Ta Baiwa Gaza Wasan Kwaikwayo Ne
  • Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoto Mai Taken “’Yancin Fadin Albarkacin Baki A Amurka: Gaskiya Da Hujjoji”

Ya kara da cewa, a shirye Sin take ta karfafa cudanya da Angola da sauran kasashen Afrika, domin kare muradun bai daya na kasashe masu tasowa da hada hannu wajen tabbatar da adalci da raba iko tsakanin kasa da kasa da tabbatar da dunkulewar tattalin arzikin duniya domin kowa ya amfana da kuma inganta gina al’umma mai makoma ta bai daya ga dukkan bil Adama.

A nasa bangare, Joao Lourenco ya ce, Sin ce kasa ta farko da ta samar da taimako mai muhimmanci ga Angola a lokacin da yakin basasar kasar ya kawo karshe da kuma yayin fama da annobar COVID-19, yana mai cewa, Angola na bayyana matukar godiyarta. Ya ce taimakon kasar Sin da hadin gwiwa da ita, sun inganta ginin ababen more rayuwa a Angola da habaka tattalin arziki da kyautata zamantakewar al’umma, lamarin da ya zama kyakkyawan misali na dangantakar moriyar juna. Ya ce kasar Angola na maraba da kamfanonin kasar Sin su zuba jari a kasar domin taimakawa ci gaban kasar da ma farfadowarta.

A wannan rana kuma, firaministan kasar Sin Li Qiang da shugaban kwamitin kula da harkokin majalisar wakilan jama’ar kasar Sin Zhao Leji sun gana da shugaban Angola bi da bi. (Fa’iza Mustapha)

Labarai Masu Nasaba

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kabilu Biyar Mafiya Tsadar Aure A Nijeriya

Next Post

An Bude Bikin Baje Kolin Kayayyakin Gida Da Na Na’Urorin Wutar Lantarki Na Yau Da Kullum A Nan Kasar Sin

Related

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

6 hours ago
Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?
Daga Birnin Sin

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

7 hours ago
Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe
Daga Birnin Sin

Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

8 hours ago
An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

9 hours ago
Sin Ta Gabatar Da Korafi Da Babbar Murya Dangane Da Kalaman Jagoran Philippines 
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gabatar Da Korafi Da Babbar Murya Dangane Da Kalaman Jagoran Philippines 

10 hours ago
Xi Ya Bukaci A Yi Dukkan Mai Yiwuwa Wajen Gudanar Da Ayyukan Bincike Da Ceto Bayan Aukuwar Ambaliya A Lardin Gansu
Daga Birnin Sin

Xi Ya Bukaci A Yi Dukkan Mai Yiwuwa Wajen Gudanar Da Ayyukan Bincike Da Ceto Bayan Aukuwar Ambaliya A Lardin Gansu

11 hours ago
Next Post
An Bude Bikin Baje Kolin Kayayyakin Gida Da Na Na’Urorin Wutar Lantarki Na Yau Da Kullum A Nan Kasar Sin

An Bude Bikin Baje Kolin Kayayyakin Gida Da Na Na’Urorin Wutar Lantarki Na Yau Da Kullum A Nan Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

August 8, 2025
Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

August 8, 2025
Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

August 8, 2025
Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

August 8, 2025
Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

August 8, 2025
Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

August 8, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

August 8, 2025
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

An Hallaka Manomi, An Kashe Shanu Da Tumakai A Wani Sabon Rikici A Bogoro

August 8, 2025
An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

August 8, 2025
Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

August 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.