• English
  • Business News
Tuesday, July 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Da Angola Sun Daga Matsayin Dangantakarsu

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Da Angola Sun Daga Matsayin Dangantakarsu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yau Jumma’a, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya gana da takwaransa na Angola Joao Lourenco a nan birnin Beijing, inda shugabannin biyu suka sanar da daga matsayin dangantakarsu zuwa ta hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare.

Xi Jinping ya bayyana cewa, Sin abokiyar dogaro ce kuma sahihiyar abokiyar hulda ga kasashen Afrika wajen kare cikakken ‘yancinsu da inganta ci gabansu da farfadowarsu. Ya ce, Sin na goyon bayan kasashen Afrika da ma Tarayyar Afrika (AU), a kokarinsu na warware batutuwan da suka shafi Afrika bisa dabarun Afrika da kuma kare tsaro da zaman lafiya a nahiyar.

  • Tallafin Da Amurka Ta Baiwa Gaza Wasan Kwaikwayo Ne
  • Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoto Mai Taken “’Yancin Fadin Albarkacin Baki A Amurka: Gaskiya Da Hujjoji”

Ya kara da cewa, a shirye Sin take ta karfafa cudanya da Angola da sauran kasashen Afrika, domin kare muradun bai daya na kasashe masu tasowa da hada hannu wajen tabbatar da adalci da raba iko tsakanin kasa da kasa da tabbatar da dunkulewar tattalin arzikin duniya domin kowa ya amfana da kuma inganta gina al’umma mai makoma ta bai daya ga dukkan bil Adama.

A nasa bangare, Joao Lourenco ya ce, Sin ce kasa ta farko da ta samar da taimako mai muhimmanci ga Angola a lokacin da yakin basasar kasar ya kawo karshe da kuma yayin fama da annobar COVID-19, yana mai cewa, Angola na bayyana matukar godiyarta. Ya ce taimakon kasar Sin da hadin gwiwa da ita, sun inganta ginin ababen more rayuwa a Angola da habaka tattalin arziki da kyautata zamantakewar al’umma, lamarin da ya zama kyakkyawan misali na dangantakar moriyar juna. Ya ce kasar Angola na maraba da kamfanonin kasar Sin su zuba jari a kasar domin taimakawa ci gaban kasar da ma farfadowarta.

A wannan rana kuma, firaministan kasar Sin Li Qiang da shugaban kwamitin kula da harkokin majalisar wakilan jama’ar kasar Sin Zhao Leji sun gana da shugaban Angola bi da bi. (Fa’iza Mustapha)

Labarai Masu Nasaba

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kabilu Biyar Mafiya Tsadar Aure A Nijeriya

Next Post

An Bude Bikin Baje Kolin Kayayyakin Gida Da Na Na’Urorin Wutar Lantarki Na Yau Da Kullum A Nan Kasar Sin

Related

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

9 hours ago
Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

10 hours ago
Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

11 hours ago
Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan
Daga Birnin Sin

Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

11 hours ago
Sin Na Bikin Cika Shekaru 88 Da Dukkan Al’ummar Kasar Ta Fara Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan
Daga Birnin Sin

Sin Na Bikin Cika Shekaru 88 Da Dukkan Al’ummar Kasar Ta Fara Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan

12 hours ago
Firaministan Kasar Sin: Kasarsa Ta Kimtsa Tsaf Wajen Inganta Aikin BRI Da Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Tare Da Habasha
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Sin: Kasarsa Ta Kimtsa Tsaf Wajen Inganta Aikin BRI Da Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Tare Da Habasha

13 hours ago
Next Post
An Bude Bikin Baje Kolin Kayayyakin Gida Da Na Na’Urorin Wutar Lantarki Na Yau Da Kullum A Nan Kasar Sin

An Bude Bikin Baje Kolin Kayayyakin Gida Da Na Na’Urorin Wutar Lantarki Na Yau Da Kullum A Nan Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

ADC: Tinubu Na Yunƙurin Raba Kawunan Masu Haɗaka Kafin Zaɓen 2027

July 8, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

July 8, 2025
Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 7, 2025
Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

July 7, 2025
Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

July 7, 2025
Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

July 7, 2025
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

July 7, 2025
Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

July 7, 2025
Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

July 7, 2025
Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

July 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.