• English
  • Business News
Thursday, August 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Da Faransa Sun Gudanar Da Taron Tattaunawa Bisa Matsayin Koli Karo Na 26 

by CGTN Hausa and Sulaiman
8 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Da Faransa Sun Gudanar Da Taron Tattaunawa Bisa Matsayin Koli Karo Na 26 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mamba a ofishin hukumar siyasa ta kwamitin kolin JKS, kana dakarta a ofishin hukumar lura da harkokin waje na kwamitin kolin jam’iyyar Wang Yi, da mashawarcin shugaban kasar Faransa kan harkokin diflomasiyya Emmanuel Bonne, sun jagoranci taron tattaunawa bisa matsayin koli na kasashen biyu karo na 26.

 

Yayin tattaunawar ta jiya Asabar a birnin Beijing fadar mulkin kasar Sin, Wang Yi, ya ce shugabannin kasashen Sin da Faransa na ci gaba da wanzar da cudanya a ‘yan shekarun baya bayan nan, sun kuma samar da wata alkiblar ci gaban dangantakar Sin da Faransa, da Sin da Turai.

  • Yadda Ake Hadin Ɗan Waken Zamani
  • ASUU Ta Fara Gangamin Shiga Yajin Aiki Yayin Da Gwamnatin Tarayya Ta Kasa Cika Alkawari

Ya ce kasar Sin a shirye take ta yi aiki tare da Faransa, wajen tabbatar da dangantakarta da Faransa ta ingiza ci gaban alakar Sin da Turai, da yaukaka yanayin zaman lafiya da daidaito a duniya baki daya.

 

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

Daga nan sai mista Wang ya gabatar da shawarwari guda 4, da suka hada da mayar da kudurorin da shugabannin kasashen 2 suka cimma matsaya a kai a matsayin alkibla, da kuma samar da karin ajandodin kyautata dangantakar sassan 2. Sai kuma ingiza hadin gwiwa, ta yadda za a yi amfani da fifikon gargajiya na sassan 2, da lalubo sabbin damammaki don ingiza hadin gwiwa bisa sabon karfi na samar da ci gaba. Na uku kuma, sassan biyu su dage wajen cin gajiya daga bikin shekarar raya al’adu da yawon bude ido na Sin da Faransa, da ingiza musayar al’ummu tsakaninsu. Kana na karshe, su hada hannu wajen goyon bayan wanzuwar cudanyar sassa daban daban.

 

A nasa tsokaci kuwa, mista Bonne, cewa ya yi Faransa na dora muhimmancin gaske ga kawancen gargajiya, da amincewa juna tsakaninta da Sin, za kuma ta nacewa manufar nan ta kasar Sin daya tak a duniya, da ci gaba da raya musaya ta kut da kut tsakanin manyan jami’ai tare da bangaren Sin, da tabbatar da cimma nasarar tsare-tsaren tattaunawa tsakaninsu. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Hatsarin Jirgin Ruwa Ya Kashe Mutane 20, ‘Yan Kasuwa Da Yara A Benue

Next Post

Ko Nawa Za A Bani Ba Zan Iya Fitowa A Matsayin Kwarto Ko Dan Daudu A Fim Ba -Dan Asabe Olala

Related

Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela
Daga Birnin Sin

Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

55 minutes ago
Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli
Daga Birnin Sin

Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

2 hours ago
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

3 hours ago
Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

4 hours ago
Xi Jinping Zai Duba Faretin Sojoji Ta Kan Titin Chang’an A Ranar Uku Ga Watan Satumba Dake Tafe
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Zai Duba Faretin Sojoji Ta Kan Titin Chang’an A Ranar Uku Ga Watan Satumba Dake Tafe

23 hours ago
Faretin Sojoji Da Sin Za Ta Gudanar Zai Shaida Muhimmancin Zaman Lafiya Da Goyon Bayan Gaskiya Da Adalci Tsakanin Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Faretin Sojoji Da Sin Za Ta Gudanar Zai Shaida Muhimmancin Zaman Lafiya Da Goyon Bayan Gaskiya Da Adalci Tsakanin Kasa Da Kasa

24 hours ago
Next Post
Ko Nawa Za A Bani Ba Zan Iya Fitowa A Matsayin Kwarto Ko Dan Daudu A Fim Ba -Dan Asabe Olala

Ko Nawa Za A Bani Ba Zan Iya Fitowa A Matsayin Kwarto Ko Dan Daudu A Fim Ba -Dan Asabe Olala

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

August 21, 2025
Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

August 21, 2025
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

August 21, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

August 21, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

August 21, 2025
NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

August 21, 2025
Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

August 21, 2025
Nijeriya Ta Kori Ƙarin ‘Yan Ƙasashen Waje 51 Da Aka Ɗaure Bisa Laifin Ta’addanci Da Zamba A Intanet

Nijeriya Ta Kori Ƙarin ‘Yan Ƙasashen Waje 51 Da Aka Ɗaure Bisa Laifin Ta’addanci Da Zamba A Intanet

August 21, 2025
Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka

Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka

August 21, 2025
Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 

Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.