ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ASUU Ta Fara Gangamin Shiga Yajin Aiki Yayin Da Gwamnatin Tarayya Ta Kasa Cika Alkawari

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
ASUU

Da akwai alamun jami’oi za su fara wani yajin aikin da za s a al’amuran koyarwa su tsaya, yayin da gwamnatin tarayya ta kasa cika alkawarin yarjejeniyar da ta sa hannu da kungiyar Malaman jami’oi ta kasa (ASUU).

Jaridar Guardian ta bada rahoton cewa kungiyar ta damu kwarai kan rashin cika alkawarin da gwamnatin tarayya ta yi da ita, na samar da Naira bilyan 200 kowace shekara wanda aka yi 2009 kudaden da za bunkasa jami’oin Nijeriya.

  • Sin Da Amurka Sun Tsawaita Yarjejeniyar Hadin Gwiwa A Fannin Raya Kimiyya Da Fasaha Da Karin Shekaru 5
  • Bankin Duniya Da Hukumar Lamuni Ke Yi Wa Tsarin Ilimin Nijeriya Zagon-kasa – ASUU

Babban jami’in kungiyar da baya son a ambaci sunansa, ya bayyana cewa kungiyar ta shiryawa tafiya yajin aikin, muddin dai gwamnati ta ki sakin kudin saboda ayyukan da ake yi masu muhimmanci da suke karkashin kungiyar, shirye suke su fara yajin aiki idan har Shugaban kasa bai sa an bada kudaden ba.

ADVERTISEMENT

Wata majiya tace matakin na, ASUU da har yanzu ba’a bayyana shi ba, ya tsaya kan rashin cika alkawarin da gwamnati ta yi na cika alkawarin da tayi tare da kungiyar a shekarar 2009 kan tsarin bukatunsu.Tsarin da aka dauka a matsayin mai canza al’amura wajen sake farfadowa da bunkasa abubuwan more rayuwa da za su taimakawa bunkasar ilimi a Jami’oin Nijeriya.

Majiyar ta ce shi shirin tafiya yajin aikin da za a yi ya dogara ne kan samun matsaya wadda ake sa ran cimmawa bayan taron da za a yi  na kwamitin zartarwa nan gaba bada dadewa ba.

LABARAI MASU NASABA

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

A wani ci gaban da aka samu wani babban kusa, na cibiyar kulawa da ayyuka ta jami’ar Jos Dr. Tunde Olagunjembi, wanda shi ne babban mai bincike ne, daga Jami’ar har ila yau kuma Malamin, ya ba Shugaban kasa shawarar kada ya yi watsi da  tsarin da aka fara wanda an yi shi ne, domin samar da kudade ga Jami’oin gwamnati saboda ci gabansu. Tsarin da aka fara an kirkiro shi ne domin a samu yin gyara kan abubuwan more rayuwa da suka lalace da kuma samar da kayan koyarwa a manyan makarantu.

Olagunjembi ya yi kira da Shugaban kasa ya ci gaba da tsarin da aka fara domin samun ci gaban yadda ake tafiyar da ilimin Jami’oi.

Ya yi kira da Shugaban kasa da kada ya bata lokaci ya amince saboda ci gaba na yin ayyukan, a makarantu da suke a karkashin tsarin.

Ya lashi takobin al’ummar Jami’a da kungiyar ASUU sun kosa da ganin yadda za a ci gaba da ayyukan a karkashin wannan mulkin.

Babban mai fada aji a Jami’a ya kara bayyana cewa samun dorewar karatu a makarantu hakan na faruwa ne sanadiyar sadaukar da kan da ‘yan kungiyar ta ASUU suka yi wadanda suka yanke shawarar za su ba Shugaban kasa lokaci domin ya samu damar tsai da hankalinsa kan ayyukan dake gabansa.

Sai dai kuma duk da hakan ya ja kunne cewar ruwa ya kusa karewa dan Kada,kamata ya yi Shugaban kasa ya dauki matakan da suka kamata wajen samar da kudade  don ci gaban ayyukan da aka fara.

Kamar yadda yace gabatar da, fara amfani samar da kudade saboda a samu aiwatar da tsarin yin ayyuka, hakan ta yiyu ne saboda yarjejeniyar da aka yi tsakanin gwamnatin tarayya da kungiyar ASUU, abin ya ta’allaka ne saboda ayi amfani da shawarwarin kwamitin ya bayar, domin ayi maganin matsalolin da ake fuskanta a manyan makarantu/ Jami’oin Nijeriya.

ASUU
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Ilimi

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Kasashen Ketare

Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

July 10, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz
Manyan Labarai

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Next Post
Nijeriya Za Ta Shiga Cikin Manyan Kasashe Masu Fitar Da Amfanin Gona A 2025 – Tinubu

Nijeriya Za Ta Shiga Cikin Manyan Kasashe Masu Fitar Da Amfanin Gona A 2025 – Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.