• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Da Honduras Sun Sanar Da Matsayarsu Bayan Taron Shugabannin Kasashen Biyu

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Da Honduras Sun Sanar Da Matsayarsu Bayan Taron Shugabannin Kasashen Biyu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A jiya Litinin ne kasashen Sin da Honduras suka fitar da sanarwar matsayar kasashen biyu bayan zantarwar shugabannin kasashen.

Sanarwar ta ce, bangarorin biyu sun amince cewa, huldar diflomasiyya tsakanin Sin da Honduras bisa ka’idar kasar Sin daya tak, ta bude wani sabon babi a tarihin dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, wanda ya dace da muhimman muradun kasashen biyu da jama’arsu.

  • Xi Da Ramaphosa Sun Tattauna Ta Wayar Tarho Kan Hulda Tsakanin Kasashen Biyu Da Rikicin Ukraine

Bangaren Honduras na ba da cikakken goyon baya da bin ka’idar kasar Sin daya tak, kuma tana adawa da “‘yancin Taiwan” ta ko wace fuska, da kuma duk wani mataki da ya saba wa ka’idar.

A karkashin tsarin hadin gwiwa na ziri daya da hanya daya, bangarorin biyu sun amince da karfafa hadin gwiwa da tsare-tsare na raya kasa, da zurfafa mu’amala da hadin gwiwa a fannoni daban daban, da aiwatar da ka’idojin tuntubar juna, da taimakawa juna, don cin moriyar juna.

Sannan gwamnatin kasar Sin ta sanya hannu kan takardar fahimtar juna, game da hadin gwiwar aiwatar da shawarar ziri daya da hanya daya tare da gwamnatin kasar Honduras.

Labarai Masu Nasaba

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Hukumar bunkasa ci gaba da aiwatar da sauye-sauye ta kasar Sin ce ta bayyana hakan a Talatar nan, inda ta ce sassan biyu za su hada karfi da karfe wajen yin tafiya tare, da bunkasa nasarar manufofin sadarwa, da raya ababen more rayuwa, da fadada cinikayya, da hade fannonin hada-hadar kudade, da musaya tsakanin al’ummun sassan biyu.

Kaza lika a cewar hukumar, karkashin takardar fahimtar junan, za a karfafa hadin gwiwa a sassa daban daban, da bunkasa cimma moriyar juna, da koyi daga wayewar kan juna, da cimma nasarorin bunkasuwa da wadata.

Game da ziyarar shugabar Honduras Iris Xiomara Castro Sarmiento take yi a kasar Sin, da dimbin yarjejeniyiyin hadin gwida da aka kulla tsakanin Sin da Honduras, da sanyin safiyar yau Talata 13 ga wata, kafofin yada labaru na kasar Honduras sun ruwaito a shafunansu cewa, an bude sabon babin raya hulda a tsakanin kasarsu da kasar Sin, tare da ambato lamba “17” sau da dama, wadda ma’anarta ita ce takardun fahimtar juna guda 17 da kasashen 2 suka daddale, a fannin hada kai a sassa daban daban.

Kasar ta Honduras, muhimmiyar kasa ce a yankin Tsakiyar Amurka, kuma sabuwar abokiyar kasar Sin ce. A ranar 26 ga watan Maris na bana, kasashen Sin da Honduras sun kafa huldar jakadanci a tsakaninsu bisa ka’idar “kasar Sin daya tak a duniya”.

Honduras ta zama ta 182, a jerin kasashen da suka kulla huldar jakadanci da kasar Sin.
A Jiya Litinin ne shugaba Xi Jinping na kasar Sin, da takwararsa ta Honduras Iris Xiomara Castro Sarmiento suka yi shawarwari, inda shugaba Xi ya jinjina wa yadda Castro ta tsai da kuduri mai matukar muhimmanci a tarihi, da kuma nuna aniyar siyasa.

A lokacin ziyarar shugaba Castro a kasar Sin, Honduras ta gabatar da rokon shiga bankin New Development Bank, kuma kasashen 2 sun amince da kaddamar da shawarwari kan yarjejeniyar ciniki cikin ‘yanci, sun kuma daddale takardar fahimtar juna kan hadin gwiwar aiwatar da shawarar ziri daya da hanya daya, tare da ba da sanarwar hadin gwiwar cimma ra’ayi daya.

Har ila yau, shugabannin kasashen 2 sun tsara shiri kan raya hulda a tsakanin kasashen 2, za kuma a kaddamar da hadin gwiwa a fannonin tattalin arziki, da ciniki, da raya al’adu da dai sauransu, a kokarin samun ci gaba tare, ta yadda al’ummun kasashen 2 za su kara samun alherai.

‘Yan kasuwan Honduras suna da yakinin cewa, jatanlanle, da kankana, da kofi na Honduras, za su samu amincewa sosai a kasar Sin. Haka kuma, Honduras na maraba da kamfanonin Sin, da su zuba jari, da shiga ayyukan raya tattalin arzikin Honduras. (Mai fassarawa: Mohammed Yahaya, Saminu Alhassan, Tasallah Yuan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Fintiri Ya Rantsar Da Bamanga Tukur Sabon SSG A Adamawa

Next Post

Mutum 100 Sun Rasu A Kifewar Wani Kwale-kwale A Jihar Kwara

Related

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

10 minutes ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

2 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

3 hours ago
Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

14 hours ago
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

18 hours ago
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

19 hours ago
Next Post
Mutum 100 Sun Rasu A Kifewar Wani Kwale-kwale A Jihar Kwara

Mutum 100 Sun Rasu A Kifewar Wani Kwale-kwale A Jihar Kwara

LABARAI MASU NASABA

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

June 6, 2025
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

June 6, 2025
Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

June 6, 2025
Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

June 6, 2025
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

June 6, 2025
aure

Kar Ki Bari Naman Sallah Ya Kashe Miki Aure Yar’uwa

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.