• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Da Honduras Sun Sanar Da Matsayarsu Bayan Taron Shugabannin Kasashen Biyu

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Da Honduras Sun Sanar Da Matsayarsu Bayan Taron Shugabannin Kasashen Biyu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A jiya Litinin ne kasashen Sin da Honduras suka fitar da sanarwar matsayar kasashen biyu bayan zantarwar shugabannin kasashen.

Sanarwar ta ce, bangarorin biyu sun amince cewa, huldar diflomasiyya tsakanin Sin da Honduras bisa ka’idar kasar Sin daya tak, ta bude wani sabon babi a tarihin dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, wanda ya dace da muhimman muradun kasashen biyu da jama’arsu.

  • Xi Da Ramaphosa Sun Tattauna Ta Wayar Tarho Kan Hulda Tsakanin Kasashen Biyu Da Rikicin Ukraine

Bangaren Honduras na ba da cikakken goyon baya da bin ka’idar kasar Sin daya tak, kuma tana adawa da “‘yancin Taiwan” ta ko wace fuska, da kuma duk wani mataki da ya saba wa ka’idar.

A karkashin tsarin hadin gwiwa na ziri daya da hanya daya, bangarorin biyu sun amince da karfafa hadin gwiwa da tsare-tsare na raya kasa, da zurfafa mu’amala da hadin gwiwa a fannoni daban daban, da aiwatar da ka’idojin tuntubar juna, da taimakawa juna, don cin moriyar juna.

Sannan gwamnatin kasar Sin ta sanya hannu kan takardar fahimtar juna, game da hadin gwiwar aiwatar da shawarar ziri daya da hanya daya tare da gwamnatin kasar Honduras.

Labarai Masu Nasaba

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba

Hukumar bunkasa ci gaba da aiwatar da sauye-sauye ta kasar Sin ce ta bayyana hakan a Talatar nan, inda ta ce sassan biyu za su hada karfi da karfe wajen yin tafiya tare, da bunkasa nasarar manufofin sadarwa, da raya ababen more rayuwa, da fadada cinikayya, da hade fannonin hada-hadar kudade, da musaya tsakanin al’ummun sassan biyu.

Kaza lika a cewar hukumar, karkashin takardar fahimtar junan, za a karfafa hadin gwiwa a sassa daban daban, da bunkasa cimma moriyar juna, da koyi daga wayewar kan juna, da cimma nasarorin bunkasuwa da wadata.

Game da ziyarar shugabar Honduras Iris Xiomara Castro Sarmiento take yi a kasar Sin, da dimbin yarjejeniyiyin hadin gwida da aka kulla tsakanin Sin da Honduras, da sanyin safiyar yau Talata 13 ga wata, kafofin yada labaru na kasar Honduras sun ruwaito a shafunansu cewa, an bude sabon babin raya hulda a tsakanin kasarsu da kasar Sin, tare da ambato lamba “17” sau da dama, wadda ma’anarta ita ce takardun fahimtar juna guda 17 da kasashen 2 suka daddale, a fannin hada kai a sassa daban daban.

Kasar ta Honduras, muhimmiyar kasa ce a yankin Tsakiyar Amurka, kuma sabuwar abokiyar kasar Sin ce. A ranar 26 ga watan Maris na bana, kasashen Sin da Honduras sun kafa huldar jakadanci a tsakaninsu bisa ka’idar “kasar Sin daya tak a duniya”.

Honduras ta zama ta 182, a jerin kasashen da suka kulla huldar jakadanci da kasar Sin.
A Jiya Litinin ne shugaba Xi Jinping na kasar Sin, da takwararsa ta Honduras Iris Xiomara Castro Sarmiento suka yi shawarwari, inda shugaba Xi ya jinjina wa yadda Castro ta tsai da kuduri mai matukar muhimmanci a tarihi, da kuma nuna aniyar siyasa.

A lokacin ziyarar shugaba Castro a kasar Sin, Honduras ta gabatar da rokon shiga bankin New Development Bank, kuma kasashen 2 sun amince da kaddamar da shawarwari kan yarjejeniyar ciniki cikin ‘yanci, sun kuma daddale takardar fahimtar juna kan hadin gwiwar aiwatar da shawarar ziri daya da hanya daya, tare da ba da sanarwar hadin gwiwar cimma ra’ayi daya.

Har ila yau, shugabannin kasashen 2 sun tsara shiri kan raya hulda a tsakanin kasashen 2, za kuma a kaddamar da hadin gwiwa a fannonin tattalin arziki, da ciniki, da raya al’adu da dai sauransu, a kokarin samun ci gaba tare, ta yadda al’ummun kasashen 2 za su kara samun alherai.

‘Yan kasuwan Honduras suna da yakinin cewa, jatanlanle, da kankana, da kofi na Honduras, za su samu amincewa sosai a kasar Sin. Haka kuma, Honduras na maraba da kamfanonin Sin, da su zuba jari, da shiga ayyukan raya tattalin arzikin Honduras. (Mai fassarawa: Mohammed Yahaya, Saminu Alhassan, Tasallah Yuan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Fintiri Ya Rantsar Da Bamanga Tukur Sabon SSG A Adamawa

Next Post

Mutum 100 Sun Rasu A Kifewar Wani Kwale-kwale A Jihar Kwara

Related

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

41 minutes ago
In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba
Daga Birnin Sin

In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba

19 hours ago
Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana

19 hours ago
Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita
Daga Birnin Sin

Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita

20 hours ago
Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin

21 hours ago
Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu
Daga Birnin Sin

Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu

22 hours ago
Next Post
Mutum 100 Sun Rasu A Kifewar Wani Kwale-kwale A Jihar Kwara

Mutum 100 Sun Rasu A Kifewar Wani Kwale-kwale A Jihar Kwara

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

July 5, 2025
Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

July 5, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

July 5, 2025
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

July 5, 2025
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

July 5, 2025
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

July 5, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

July 5, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

July 5, 2025
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.