ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Da Honduras Sun Sanar Da Matsayarsu Bayan Taron Shugabannin Kasashen Biyu

by CMG Hausa
3 years ago
Honduras

A jiya Litinin ne kasashen Sin da Honduras suka fitar da sanarwar matsayar kasashen biyu bayan zantarwar shugabannin kasashen.

Sanarwar ta ce, bangarorin biyu sun amince cewa, huldar diflomasiyya tsakanin Sin da Honduras bisa ka’idar kasar Sin daya tak, ta bude wani sabon babi a tarihin dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, wanda ya dace da muhimman muradun kasashen biyu da jama’arsu.

  • Xi Da Ramaphosa Sun Tattauna Ta Wayar Tarho Kan Hulda Tsakanin Kasashen Biyu Da Rikicin Ukraine

Bangaren Honduras na ba da cikakken goyon baya da bin ka’idar kasar Sin daya tak, kuma tana adawa da “‘yancin Taiwan” ta ko wace fuska, da kuma duk wani mataki da ya saba wa ka’idar.

ADVERTISEMENT

A karkashin tsarin hadin gwiwa na ziri daya da hanya daya, bangarorin biyu sun amince da karfafa hadin gwiwa da tsare-tsare na raya kasa, da zurfafa mu’amala da hadin gwiwa a fannoni daban daban, da aiwatar da ka’idojin tuntubar juna, da taimakawa juna, don cin moriyar juna.

Sannan gwamnatin kasar Sin ta sanya hannu kan takardar fahimtar juna, game da hadin gwiwar aiwatar da shawarar ziri daya da hanya daya tare da gwamnatin kasar Honduras.

LABARAI MASU NASABA

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Hukumar bunkasa ci gaba da aiwatar da sauye-sauye ta kasar Sin ce ta bayyana hakan a Talatar nan, inda ta ce sassan biyu za su hada karfi da karfe wajen yin tafiya tare, da bunkasa nasarar manufofin sadarwa, da raya ababen more rayuwa, da fadada cinikayya, da hade fannonin hada-hadar kudade, da musaya tsakanin al’ummun sassan biyu.

Kaza lika a cewar hukumar, karkashin takardar fahimtar junan, za a karfafa hadin gwiwa a sassa daban daban, da bunkasa cimma moriyar juna, da koyi daga wayewar kan juna, da cimma nasarorin bunkasuwa da wadata.

Game da ziyarar shugabar Honduras Iris Xiomara Castro Sarmiento take yi a kasar Sin, da dimbin yarjejeniyiyin hadin gwida da aka kulla tsakanin Sin da Honduras, da sanyin safiyar yau Talata 13 ga wata, kafofin yada labaru na kasar Honduras sun ruwaito a shafunansu cewa, an bude sabon babin raya hulda a tsakanin kasarsu da kasar Sin, tare da ambato lamba “17” sau da dama, wadda ma’anarta ita ce takardun fahimtar juna guda 17 da kasashen 2 suka daddale, a fannin hada kai a sassa daban daban.

Kasar ta Honduras, muhimmiyar kasa ce a yankin Tsakiyar Amurka, kuma sabuwar abokiyar kasar Sin ce. A ranar 26 ga watan Maris na bana, kasashen Sin da Honduras sun kafa huldar jakadanci a tsakaninsu bisa ka’idar “kasar Sin daya tak a duniya”.

Honduras ta zama ta 182, a jerin kasashen da suka kulla huldar jakadanci da kasar Sin.
A Jiya Litinin ne shugaba Xi Jinping na kasar Sin, da takwararsa ta Honduras Iris Xiomara Castro Sarmiento suka yi shawarwari, inda shugaba Xi ya jinjina wa yadda Castro ta tsai da kuduri mai matukar muhimmanci a tarihi, da kuma nuna aniyar siyasa.

A lokacin ziyarar shugaba Castro a kasar Sin, Honduras ta gabatar da rokon shiga bankin New Development Bank, kuma kasashen 2 sun amince da kaddamar da shawarwari kan yarjejeniyar ciniki cikin ‘yanci, sun kuma daddale takardar fahimtar juna kan hadin gwiwar aiwatar da shawarar ziri daya da hanya daya, tare da ba da sanarwar hadin gwiwar cimma ra’ayi daya.

Har ila yau, shugabannin kasashen 2 sun tsara shiri kan raya hulda a tsakanin kasashen 2, za kuma a kaddamar da hadin gwiwa a fannonin tattalin arziki, da ciniki, da raya al’adu da dai sauransu, a kokarin samun ci gaba tare, ta yadda al’ummun kasashen 2 za su kara samun alherai.

‘Yan kasuwan Honduras suna da yakinin cewa, jatanlanle, da kankana, da kofi na Honduras, za su samu amincewa sosai a kasar Sin. Haka kuma, Honduras na maraba da kamfanonin Sin, da su zuba jari, da shiga ayyukan raya tattalin arzikin Honduras. (Mai fassarawa: Mohammed Yahaya, Saminu Alhassan, Tasallah Yuan)

Honduras
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
Daga Birnin Sin

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
Daga Birnin Sin

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines
Daga Birnin Sin

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Next Post
Mutum 100 Sun Rasu A Kifewar Wani Kwale-kwale A Jihar Kwara

Mutum 100 Sun Rasu A Kifewar Wani Kwale-kwale A Jihar Kwara

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

June 13, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.