• English
  • Business News
Monday, May 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Da Kasashen Afirka Na Kara Karfafa Kawance Da Bunkasa Damammakin Hadin Gwiwa

by CGTN Hausa and Sulaiman
9 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Da Kasashen Afirka Na Kara Karfafa Kawance Da Bunkasa Damammakin Hadin Gwiwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Nan da ’yan kwanaki kalilan, shugabannin Sin da na kasashen Afirka za su sake haduwa a birnin Beijing, inda ake sa ran sake sabunta kawance, da tattauna tsare-tsaren bunkasa hadin gwiwa. Masharhanta na ganin wannan taro zai share fagen zurfafa amincewa da juna, da daga martabar hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka, tare da karfafa rungumar manufofi da sassan biyu suka amincewa, ta yadda za a kai ga gina al’ummar Sin da Afirka mai makomar bai daya bisa matsayin koli.

 

Idan mun yi la’akari da matakai daban daban da bangaren Sin ke dauka, musamman yadda shugaban kasar Xi Jinping ke dora muhimmancin gaske ga hadin gwiwar Sin da Afirka, ta hanyar fitar da tsare-tsare na raya kawancen su, da gabatar da manufofin cimma nasarori daki-daki, ma iya cewa Sin da Afirka na tunkarar wata makoma mai haske ta cimma manyan nasarori yadda ya kamata.

  • Ƙasar Sin Ta Ƙaddamar Da Ƙayataccen Shirin Bidiyo Na “Kwaɗon Baka” A Nijeriya
  • Sin Da Afirka Aminai Ne Wajen Neman Zamanantar Da Kansu

Idan mun waiwayi baya, muna iya tuna ziyarar da shugaba Xi ya gudanar a nahiyar Afirka a watan Maris na shekarar 2013, inda ya gabatar da wasu manufofi masu nasaba da bunkasa alakar Sin da nahiyar Afirka. Kana a yayin taron dandalin bunkasa hadin gwiwar Sin da Afirka na FOCAC, wanda ya gudana a birnin Johannesburg na Afirka ta kudu a watan Disambar 2015, shugaban na Sin ya bayyana shirin aiwatar da wasu manyan manufofin hadin gwiwa da Afirka har guda 10, kana sassan biyu suka amince da daga matsayin kawancensu zuwa dangantakar abokantaka ta hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare daga dukkanin fannoni. Kuma shekaru 3 bayan hakan a shekarar 2018, shugaban na Sin ya karbi bakuncin taron FOCAC na birnin Beijing, inda ya ayyana manufar nan ta kara kusantar juna tsakanin Sin da kasashen Afirka don kaiwa ga gina al’ummar sassan biyu mai makomar bai daya a sabon zamani.

 

Labarai Masu Nasaba

A Koyi Darasi Daga Tarihi

Kada A Bata Ran Mahaifiya

Dukkanin wadannan da wasu makamantansu da dama, matakai ne dake nuna yadda har kullum Sin ke nacewa burin cimma nasarar hadin gwiwa da kasashen Afirka.

 

Yayin da kasashe masu tasowa ke kara fahimtar muhimmancin tafiya tare, Sin da kasashen Afirka na kara ingiza hadin kai da cimma moriya tare, lamarin dake zama wani karfi na kafuwar duniya mai makomar bai daya, wadda za ta amfani daukacin al’ummunta ta fuskar raya tattalin arziki da zamantakewa, da dunkulewa guri guda, kamar dai yadda a ko da yaushe taron dandalin FOCAC ke kara ingiza wannan manufa.(Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zargin Luwaɗi Da Maɗigo: Gwamnatin Bauchi Ta Gayyaci Sheikh Gadon-Kaya Don Ƙarin Haske

Next Post

Adadin Masu Amfani Da Intanet A Kasar Sin Ya Kai Biliyan 1.1

Related

A Koyi Darasi Daga Tarihi
Daga Birnin Sin

A Koyi Darasi Daga Tarihi

3 hours ago
Kada A Bata Ran Mahaifiya
Daga Birnin Sin

Kada A Bata Ran Mahaifiya

4 hours ago
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Akasarin Jama’a Da Cudanyar Cinikayya Tare Da Sin Fiye Da Amurka
Daga Birnin Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Akasarin Jama’a Da Cudanyar Cinikayya Tare Da Sin Fiye Da Amurka

6 hours ago
Wang Yi: Ziyarar Shugaba Xi A Rasha Ta Kara Yaukaka Kawance Da Daidaito Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Wang Yi: Ziyarar Shugaba Xi A Rasha Ta Kara Yaukaka Kawance Da Daidaito Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

8 hours ago
Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Bude Taron Ministoci Na Dandalin Sin Da CELAC Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Bude Taron Ministoci Na Dandalin Sin Da CELAC Karo Na 4

8 hours ago
Sin Na Fatan India Da Pakistan Za Su Kaucewa Kara Rura Wutar Tashin Hankali
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan India Da Pakistan Za Su Kaucewa Kara Rura Wutar Tashin Hankali

10 hours ago
Next Post
Adadin Masu Amfani Da Intanet A Kasar Sin Ya Kai Biliyan 1.1

Adadin Masu Amfani Da Intanet A Kasar Sin Ya Kai Biliyan 1.1

LABARAI MASU NASABA

A Koyi Darasi Daga Tarihi

A Koyi Darasi Daga Tarihi

May 11, 2025
Kada A Bata Ran Mahaifiya

Kada A Bata Ran Mahaifiya

May 11, 2025
Sojoji Sun Cafke Dillalan Sayar Da Bindigu A Filato

Sojoji Sun Cafke Dillalan Sayar Da Bindigu A Filato

May 11, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Akasarin Jama’a Da Cudanyar Cinikayya Tare Da Sin Fiye Da Amurka

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Akasarin Jama’a Da Cudanyar Cinikayya Tare Da Sin Fiye Da Amurka

May 11, 2025
Ɗan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato

Ɗan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato

May 11, 2025
Wang Yi: Ziyarar Shugaba Xi A Rasha Ta Kara Yaukaka Kawance Da Daidaito Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Wang Yi: Ziyarar Shugaba Xi A Rasha Ta Kara Yaukaka Kawance Da Daidaito Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

May 11, 2025
Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Bude Taron Ministoci Na Dandalin Sin Da CELAC Karo Na 4

Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Bude Taron Ministoci Na Dandalin Sin Da CELAC Karo Na 4

May 11, 2025
2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

INEC Na Samun Matsin Lamba Don Kar Ta Yi Wa TNN Rajista — Kakakinta

May 11, 2025
Minista Ya Ƙaddamar Da Yekuwar Wayar da Kan Ɗalibai Kan Kafofin Sadarwa

Minista Ya Ƙaddamar Da Yekuwar Wayar da Kan Ɗalibai Kan Kafofin Sadarwa

May 11, 2025
Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu

Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu

May 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.