• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Da Kasashen Afirka Na Kara Karfafa Kawance Da Bunkasa Damammakin Hadin Gwiwa

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Sin

Nan da ’yan kwanaki kalilan, shugabannin Sin da na kasashen Afirka za su sake haduwa a birnin Beijing, inda ake sa ran sake sabunta kawance, da tattauna tsare-tsaren bunkasa hadin gwiwa. Masharhanta na ganin wannan taro zai share fagen zurfafa amincewa da juna, da daga martabar hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka, tare da karfafa rungumar manufofi da sassan biyu suka amincewa, ta yadda za a kai ga gina al’ummar Sin da Afirka mai makomar bai daya bisa matsayin koli.

 

Idan mun yi la’akari da matakai daban daban da bangaren Sin ke dauka, musamman yadda shugaban kasar Xi Jinping ke dora muhimmancin gaske ga hadin gwiwar Sin da Afirka, ta hanyar fitar da tsare-tsare na raya kawancen su, da gabatar da manufofin cimma nasarori daki-daki, ma iya cewa Sin da Afirka na tunkarar wata makoma mai haske ta cimma manyan nasarori yadda ya kamata.

  • Ƙasar Sin Ta Ƙaddamar Da Ƙayataccen Shirin Bidiyo Na “Kwaɗon Baka” A Nijeriya
  • Sin Da Afirka Aminai Ne Wajen Neman Zamanantar Da Kansu

Idan mun waiwayi baya, muna iya tuna ziyarar da shugaba Xi ya gudanar a nahiyar Afirka a watan Maris na shekarar 2013, inda ya gabatar da wasu manufofi masu nasaba da bunkasa alakar Sin da nahiyar Afirka. Kana a yayin taron dandalin bunkasa hadin gwiwar Sin da Afirka na FOCAC, wanda ya gudana a birnin Johannesburg na Afirka ta kudu a watan Disambar 2015, shugaban na Sin ya bayyana shirin aiwatar da wasu manyan manufofin hadin gwiwa da Afirka har guda 10, kana sassan biyu suka amince da daga matsayin kawancensu zuwa dangantakar abokantaka ta hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare daga dukkanin fannoni. Kuma shekaru 3 bayan hakan a shekarar 2018, shugaban na Sin ya karbi bakuncin taron FOCAC na birnin Beijing, inda ya ayyana manufar nan ta kara kusantar juna tsakanin Sin da kasashen Afirka don kaiwa ga gina al’ummar sassan biyu mai makomar bai daya a sabon zamani.

 

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya

Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

Dukkanin wadannan da wasu makamantansu da dama, matakai ne dake nuna yadda har kullum Sin ke nacewa burin cimma nasarar hadin gwiwa da kasashen Afirka.

 

Yayin da kasashe masu tasowa ke kara fahimtar muhimmancin tafiya tare, Sin da kasashen Afirka na kara ingiza hadin kai da cimma moriya tare, lamarin dake zama wani karfi na kafuwar duniya mai makomar bai daya, wadda za ta amfani daukacin al’ummunta ta fuskar raya tattalin arziki da zamantakewa, da dunkulewa guri guda, kamar dai yadda a ko da yaushe taron dandalin FOCAC ke kara ingiza wannan manufa.(Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya

October 10, 2025
Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

October 10, 2025
An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal
Daga Birnin Sin

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

October 9, 2025
Next Post
Adadin Masu Amfani Da Intanet A Kasar Sin Ya Kai Biliyan 1.1

Adadin Masu Amfani Da Intanet A Kasar Sin Ya Kai Biliyan 1.1

LABARAI MASU NASABA

Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

2027: INEC Ta Nemi A Gaggauta Amincewa Da Ƙudirin Sake Fasalin Tsarin Zaɓe

October 10, 2025
Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya

Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya

October 10, 2025
Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

October 10, 2025
Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

October 10, 2025
An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 

An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 

October 10, 2025
Nijeriya

Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara

October 10, 2025
Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

October 10, 2025
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)

Yadda Za A Magance Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya – TRCN

October 10, 2025
Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

October 10, 2025
Sin

Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

October 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.