• English
  • Business News
Wednesday, June 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Da Kasashen Larabawa Za Su Gaggauta Aikin Kafa Al’umma Mai Makomar Bai Daya

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Da Kasashen Larabawa Za Su Gaggauta Aikin Kafa Al’umma Mai Makomar Bai Daya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Dalilin Da Ya Sa Sin Ta Samu Bunkasar Tattalin Arziki Mai Dorewa Duk Da Kalubalolin Da Ake Fuskanta A Duniya

Xi Da Shugabannin Kasashe 5 Na Tsakiyar Asiya Sun Halarci Bikin Rattaba Hannu

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya halarci bikin bude taron ministoci karo na 10 na dandalin tattauna hadin kan Sin da kasashen Larabawa a jiya Alhamis, inda ya sanar da cewa, kasar Sin za ta kira taron koli karo na 2 tsakanin Sin da kasashen Larabawa a shekarar 2026, kuma tabbas, zai kasance sabon babin dangantakar dake tsakanin kasar Sin da kasashen Larabawa. Haka kuma, ya bayyana ra’ayinsa game da yadda za a ci gaba da raya dangantakar dake tsakanin bangarorin biyu, yayin da ya gabatar da fannoni guda biyar da za su hada kai a nan gaba, domin gaggauta aikin kafa al’umma mai makomar bai daya a tsakanin Sin da kasashen Larabawa.

A bana, ake cika shekaru 20 da kafuwar dandalin tattauna hadin gwiwar kasar Sin da kasashen Larabawa. Cikin shekaru 20 da suka gabata, bangarorin biyu sun raya dangantakar dake tsakaninsu inda ya zama abin koyi ta fuskar hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa. Yanzu, ana aiwatar da shirin “Ziri daya da hanya daya” a cikin kasashen Larabawa 22, lamarin da ya tallafawa al’ummomin bangarorin biyu kimanin biliyan 2.

  • Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Tunisia Kais Saied
  • Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Tunisia Kais Saied

Kuma an lura cewa, a wannan karo, shugabannin kasashe 4 da suka hada da Bahrain, da Masar, da Tunisiya, da Hadaddiyar Daular Larabawa wato UAE, sun halarci bikin bude taron ministocin. Dangane da wannan lamari, Jaridar Arab Weekly ta fidda wani sharhi dake cewa, halartar shugabannin kasashen hudu taron, ya nuna jagorancin shugabannin Sin da kasashen Larabawa kan hadin gwiwar dake tsakaninsu, ya kuma nuna aniya da fatan shugabannin Sin da Kasashen Larabawa ta karfafa hadin gwiwarsu da kuma raya dangantakar dake tsakaninsu zuwa sabon matsayi. A yayin taron na wannan karo, an kuma gabatar da sanarwar hadin gwiwa ta Sin da kasashen Larabawa game da batun Falesdinu, inda aka yi kiran kawo karshen riciki a yankin Gaza, da kuma warware matsalar daga dukkanin fannoni, kuma bisa adalci.

Taron na wannan karo ya kasance sabon mafari ga kasar Sin da kasashen Larabawa, don haka ya kamata su dauki matakai masu dacewa yayin aiwatar da ayyukansu yadda ya kamata, domin shimfida zaman lafiya da zaman karko ga duniyarmu dake cikin halin sauye-sauye. (Mai Fassarawa: Maryam Yang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Fasahar ‘HereafterAI’ Ke Ba Da Damar Magana Da Muryar Mutum Bayan Mutuwarsa

Next Post

Hanyar Ci Gaba Da Gwamnatin Tinubu Za Ta Bi, Ba Takure Tunani Wuri Guda Ba – Obasanjo

Related

Dalilin Da Ya Sa Sin Ta Samu Bunkasar Tattalin Arziki Mai Dorewa Duk Da Kalubalolin Da Ake Fuskanta A Duniya
Daga Birnin Sin

Dalilin Da Ya Sa Sin Ta Samu Bunkasar Tattalin Arziki Mai Dorewa Duk Da Kalubalolin Da Ake Fuskanta A Duniya

6 hours ago
Xi Da Shugabannin Kasashe 5 Na Tsakiyar Asiya Sun Halarci Bikin Rattaba Hannu
Daga Birnin Sin

Xi Da Shugabannin Kasashe 5 Na Tsakiyar Asiya Sun Halarci Bikin Rattaba Hannu

7 hours ago
Sin Ta Cimma Sabuwar Nasarar Bincike Duniyar Wata
Daga Birnin Sin

Sin Ta Cimma Sabuwar Nasarar Bincike Duniyar Wata

7 hours ago
An Gudanar Da Bikin Mu’amalar Jama’a Da Al’adu A Tsakanin Sin Da Tsakiyar Asiya A Astana
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Bikin Mu’amalar Jama’a Da Al’adu A Tsakanin Sin Da Tsakiyar Asiya A Astana

9 hours ago
Masu Karanta Adabin Shafin Intanet Na Sin Sun Kai Miliyan 575
Daga Birnin Sin

Masu Karanta Adabin Shafin Intanet Na Sin Sun Kai Miliyan 575

11 hours ago
Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53
Daga Birnin Sin

Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53

11 hours ago
Next Post
Obasanjo

Hanyar Ci Gaba Da Gwamnatin Tinubu Za Ta Bi, Ba Takure Tunani Wuri Guda Ba – Obasanjo

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Da Ya Sa Sin Ta Samu Bunkasar Tattalin Arziki Mai Dorewa Duk Da Kalubalolin Da Ake Fuskanta A Duniya

Dalilin Da Ya Sa Sin Ta Samu Bunkasar Tattalin Arziki Mai Dorewa Duk Da Kalubalolin Da Ake Fuskanta A Duniya

June 17, 2025
An Kama Mutane 26 Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Kogi

An Kama Mutane 26 Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Kogi

June 17, 2025
Xi Da Shugabannin Kasashe 5 Na Tsakiyar Asiya Sun Halarci Bikin Rattaba Hannu

Xi Da Shugabannin Kasashe 5 Na Tsakiyar Asiya Sun Halarci Bikin Rattaba Hannu

June 17, 2025
Sin Ta Cimma Sabuwar Nasarar Bincike Duniyar Wata

Sin Ta Cimma Sabuwar Nasarar Bincike Duniyar Wata

June 17, 2025
Majalisar Wakilai Ta Fara Binciken Yadda Aka Raba Naira Tiriliyan 1.12 Kan Shirin Lamuni Ga Manoma Da Masana’antu

Majalisar Wakilai Ta Fara Binciken Yadda Aka Raba Naira Tiriliyan 1.12 Kan Shirin Lamuni Ga Manoma Da Masana’antu

June 17, 2025
An Gudanar Da Bikin Mu’amalar Jama’a Da Al’adu A Tsakanin Sin Da Tsakiyar Asiya A Astana

An Gudanar Da Bikin Mu’amalar Jama’a Da Al’adu A Tsakanin Sin Da Tsakiyar Asiya A Astana

June 17, 2025
Kaftin Din Super Eagles, Ahmed Musa Ya Bukaci A Gaggauta Kawo Karshen Kashe-kashen Rayuka A Benuwe

Kaftin Din Super Eagles, Ahmed Musa Ya Bukaci A Gaggauta Kawo Karshen Kashe-kashen Rayuka A Benuwe

June 17, 2025
Masu Karanta Adabin Shafin Intanet Na Sin Sun Kai Miliyan 575

Masu Karanta Adabin Shafin Intanet Na Sin Sun Kai Miliyan 575

June 17, 2025
Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53

Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53

June 17, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

2025 UTME: Cibiyoyin Zana Jarabawar 11 Na Fuskantar Barazanar Dakatarwa – JAMB

June 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.