• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Da Saudiyya Abokai Ne Na Gaskiya Bisa Manyan Tsare-tsare

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Da Saudiyya Abokai Ne Na Gaskiya Bisa Manyan Tsare-tsare
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Shugabannin kasashen Sin da Saudiyya, sun daddale yerjejeniyar raya dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare a dukkan fannoni a tsakanin kasashen 2, inda suka amince da daga matsayin shugaban kwamitin hadin gwiwa na manyan jami’an kasashen Sin da Saudiyya zuwa matsayin firaminista, kana Sin ta amince da maida kasar Saudiyya a matsayin wurin yawon shakatawa da Sinawa za su rika zuwa cikin tawaga, kuma kasar Saudiyya ta yi maraba da karin kamfanonin Sin da su shiga aikin raya masana’antun kasar.

A ranar 8 ga wannan wata ne, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da Sarki Salman bin Abdul Aziz Al Saud na masarautar Saudiyya, kana ya yi shawarwari tare da firaministan kasar kuma yarima Muhammad bin Salman bin Abdel Aziz Al Saud. Inda bangarorin biyu suka cimma daidaito kan yadda za a sa kaimi ga raya dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare a dukkan fannoni a tsakaninsu. Babban editan jaridar Al Riyadh ta kasar Saudiyya Hani Wafa ya wallafa wani sharhi dake cewa, wannan ziyara za ta sa kaimi ga raya hadin gwiwar dake tsakanin Saudiyya da Sin a dukkan fannoni zuwa wani sabon mataki, hakan zai taimaka wajen samar da kyakkyawar makoma kan dangantakarsu.

  • Sin Ta Yi Nasarar Harba Tauraron Dan Adam Na Tattara Bayanan Kasa

A jawabinsa, Sarki Salman na Saidiyya ya bayyana cewa, moriyar Sin ita ce moriyar Saudiyya. Wannan magana ta jawo hankalin kafofin watsa labaru da dama. Yayin ziyarar shugaba Xi, bangarorin biyu sun nuna goyon baya ga juna kan harkokin siyasa. Shugaba Xi Jinping ya jaddada cewa, Sin tana goyon bayan kasar Saudiyya da ta ci gaba da bin hanyar bunkasa kasa bisa yanayin kasar. Firaminista kuma yarima Muhammad shi ma ya nuna goyon baya ga kasar Sin sosai. A yanayin tinkarar sauye-sauye da kasa da kasa da yankuna ke fuskanta, Sin da Saudiyya sun nuna goyon baya ga juna kan manyan batutuwan dake shafar moriyarsu, hakan zai tabbatar da raya dangantakar dake tsakaninsu a sabon zamani.

Zurfafa dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare a dukkan fannoni a tsakanin Sin da Saudiyya zai kawo kyakkyawar fata ga jama’arsu, kana zai samar da karin gudummawa wajen tabbatar da zaman lafiya a yankin gabas ta tsakiya da kuma samun bunkasuwa da wadata a duniya baki daya. (Zainab)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Za A Rataye Wani Da Ya Yi Wa Budurwa Fyade A Ekiti

Next Post

Sheikh Awad Moawad Dan Kasar Saudiyya Mai Shekaru 134 Ya Rasu

Related

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

1 hour ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

1 hour ago
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

18 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

18 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

20 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

23 hours ago
Next Post
Sheikh Awad Moawad Dan Kasar Saudiyya Mai Shekaru 134 Ya Rasu

Sheikh Awad Moawad Dan Kasar Saudiyya Mai Shekaru 134 Ya Rasu

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Saudiyya

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.