ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, August 3, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Da Saudiyya Abokai Ne Na Gaskiya Bisa Manyan Tsare-tsare

by CMG Hausa
4 years ago
Saudiyya

LABARAI MASU NASABA

Babban Bankin Sin: Za A Ci Gaba Da Gudanar Da Matakan Saukaka Harkokin Kudade

Yawan Tikitin Kallon Fina Finan Sin Da Aka Sayar A 2026 Ya Zarce Yuan Biliyan 23

Shugabannin kasashen Sin da Saudiyya, sun daddale yerjejeniyar raya dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare a dukkan fannoni a tsakanin kasashen 2, inda suka amince da daga matsayin shugaban kwamitin hadin gwiwa na manyan jami’an kasashen Sin da Saudiyya zuwa matsayin firaminista, kana Sin ta amince da maida kasar Saudiyya a matsayin wurin yawon shakatawa da Sinawa za su rika zuwa cikin tawaga, kuma kasar Saudiyya ta yi maraba da karin kamfanonin Sin da su shiga aikin raya masana’antun kasar.

A ranar 8 ga wannan wata ne, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da Sarki Salman bin Abdul Aziz Al Saud na masarautar Saudiyya, kana ya yi shawarwari tare da firaministan kasar kuma yarima Muhammad bin Salman bin Abdel Aziz Al Saud. Inda bangarorin biyu suka cimma daidaito kan yadda za a sa kaimi ga raya dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare a dukkan fannoni a tsakaninsu. Babban editan jaridar Al Riyadh ta kasar Saudiyya Hani Wafa ya wallafa wani sharhi dake cewa, wannan ziyara za ta sa kaimi ga raya hadin gwiwar dake tsakanin Saudiyya da Sin a dukkan fannoni zuwa wani sabon mataki, hakan zai taimaka wajen samar da kyakkyawar makoma kan dangantakarsu.

  • Sin Ta Yi Nasarar Harba Tauraron Dan Adam Na Tattara Bayanan Kasa

A jawabinsa, Sarki Salman na Saidiyya ya bayyana cewa, moriyar Sin ita ce moriyar Saudiyya. Wannan magana ta jawo hankalin kafofin watsa labaru da dama. Yayin ziyarar shugaba Xi, bangarorin biyu sun nuna goyon baya ga juna kan harkokin siyasa. Shugaba Xi Jinping ya jaddada cewa, Sin tana goyon bayan kasar Saudiyya da ta ci gaba da bin hanyar bunkasa kasa bisa yanayin kasar. Firaminista kuma yarima Muhammad shi ma ya nuna goyon baya ga kasar Sin sosai. A yanayin tinkarar sauye-sauye da kasa da kasa da yankuna ke fuskanta, Sin da Saudiyya sun nuna goyon baya ga juna kan manyan batutuwan dake shafar moriyarsu, hakan zai tabbatar da raya dangantakar dake tsakaninsu a sabon zamani.

ADVERTISEMENT

Zurfafa dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare a dukkan fannoni a tsakanin Sin da Saudiyya zai kawo kyakkyawar fata ga jama’arsu, kana zai samar da karin gudummawa wajen tabbatar da zaman lafiya a yankin gabas ta tsakiya da kuma samun bunkasuwa da wadata a duniya baki daya. (Zainab)

Saudiyya
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Babban Bankin Sin: Za A Ci Gaba Da Gudanar Da Matakan Saukaka Harkokin Kudade
Daga Birnin Sin

Babban Bankin Sin: Za A Ci Gaba Da Gudanar Da Matakan Saukaka Harkokin Kudade

August 2, 2026
Yawan Tikitin Kallon Fina Finan Sin Da Aka Sayar A 2026 Ya Zarce Yuan Biliyan 23
Daga Birnin Sin

Yawan Tikitin Kallon Fina Finan Sin Da Aka Sayar A 2026 Ya Zarce Yuan Biliyan 23

August 2, 2026
Sin Ta Fitar Da Shirin Shekaru 5 Na Daukaka Tsarin Tallata Da Samar Da Kayayyaki Domin Kyautata Hidimomi A Kauyuka
Daga Birnin Sin

Sin Ta Fitar Da Shirin Shekaru 5 Na Daukaka Tsarin Tallata Da Samar Da Kayayyaki Domin Kyautata Hidimomi A Kauyuka

August 2, 2026
Next Post
Sheikh Awad Moawad Dan Kasar Saudiyya Mai Shekaru 134 Ya Rasu

Sheikh Awad Moawad Dan Kasar Saudiyya Mai Shekaru 134 Ya Rasu

LABARAI MASU NASABA

DSS

DSS Da ‘Yan Sa-kai Sun Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Da Mayaƙansa Sama Da 60 A Katsina

August 3, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Iran Ta Musanta Iƙirarin Trump Kan Sabbin Tattaunawa da Amurka

August 3, 2026
Zamfara

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji Shida, Sun Sace Mutane 75 A Zamfara

August 3, 2026
Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

August 3, 2026
Kamfanin Abinci Na ‘BUA Foods’ Ya Samu Ribar ₦292.27bn A Rabin Farkon 2026

Kamfanin Abinci Na ‘BUA Foods’ Ya Samu Ribar ₦292.27bn A Rabin Farkon 2026

August 3, 2026
Saudiyya

WAFCON 2026: Ƴan Wasan Nijeriya 2 Ba Zasu Buga Wasan Ƙarshe Na Rukunin C Ba

August 2, 2026
Babban Bankin Sin: Za A Ci Gaba Da Gudanar Da Matakan Saukaka Harkokin Kudade

Babban Bankin Sin: Za A Ci Gaba Da Gudanar Da Matakan Saukaka Harkokin Kudade

August 2, 2026
Yawan Tikitin Kallon Fina Finan Sin Da Aka Sayar A 2026 Ya Zarce Yuan Biliyan 23

Yawan Tikitin Kallon Fina Finan Sin Da Aka Sayar A 2026 Ya Zarce Yuan Biliyan 23

August 2, 2026
Saudiyya

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Ceto Mutane 9 A Zamfara

August 2, 2026
Sin Ta Fitar Da Shirin Shekaru 5 Na Daukaka Tsarin Tallata Da Samar Da Kayayyaki Domin Kyautata Hidimomi A Kauyuka

Sin Ta Fitar Da Shirin Shekaru 5 Na Daukaka Tsarin Tallata Da Samar Da Kayayyaki Domin Kyautata Hidimomi A Kauyuka

August 2, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.