ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Rataye Wani Da Ya Yi Wa Budurwa Fyade A Ekiti

by Sabo Ahmad
4 years ago
Fyade

Wata babbar kotun jihar Ekiti, da ke Ado Ekiti ta yanke wa wani mutum mai kimanin shekara 24, mai suna Segun Iwaetan, hukuncin kisa ta hanyar rataya, saboda kama shi da laifin fyaden da ya yi wa wata makociyarsa mai shekara 20, da kuma kama shi da bindiga guda biyu.

An tuhumi wanda ake zargin ne da laifuka guda bakwai wadanda dukkansu ke da alaka da fyade da mallakar bindiga da kuma zama dan kungiyar asiri.

  • Kotu: Mutane 33 Aka Yi Wa Hukunci Daga 11,000 Da Ake Zargin Sun Aikata Fyade A Nijeriya 

Kamar yadda takardar tuhumar ta nuna, “Segun Iwaetan da Atila Iwaetan (wanda a halin yanzu ya gudu), sun hada baki wajen balle gida da sata a shagon Olayemi Oyerinde, suka kwashi kaya wadanda aka kiyasta kudinsu fiye da naira miliyan 1.8.

ADVERTISEMENT

Haka kuma wadanda ake zargin ya yi wa wata mace mai kimanin shekara 20 da ke zaune a Odo Ado, Ado Ekiti fyade, an kuma kama shi da laifin mallakar bindiga guda biyu da kuma laifin zama dan kungiyar asiri.

Wadda aka yi wa fyaden ta ce, “wannan da ya yi min fyadrn makocina ne. A wannan rana da zai yi min fyaden, sai ya shigo dakina da tsakar dare, ina kwance ya tashe ni, ya nuna min bindiga kuma ya ce, idan na yi ihu zai harbe ni. Sai ya ce in cire kayana , a nan ne ya yi min fyade. Bayan ya gama, sai ya roke ni cewa in yafe masa. Ni kuma na ce, na ki.”
Dansanda mai gabatar da kara, Albert Adeyemi, ya gabatar da shaidu guda biyar da suka tabbatar da bayanin wadda aka yi wa fyaden. Lauyan wanda ake zargin, bai kira shaida ko daya ba.

LABARAI MASU NASABA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

Da yake yanke hukunci, mai shari’a Adeniyi Familoni, bayan tabbatar da laifin da ake zargi, ya yanke hukunci kan hada baki wajen aikata laifi da mallakar makami ba bisa ka’ida ba, na shekara 12 a kurkuku, ba tare da zabin tara ba.

“Dangane da batun fyade kuwa, kotun ta yanke hukuncin daurin rai-da-rai,” Sai kuma shiga kungiyar asiri ta Eiye, alkalin ya gaya wa wanda aka gabatar, cewa “hukunci na karshe shi ne na kisa ta hanyar rataya.”

Fyade
Sabo Ahmad
+ postsBio
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    An Gurfanar Da Mutum 3 Bisa Laifin Lakada Wa Wani Duka Har Lahira
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    Dalilin Da Ya Sa Kotu Ta Tasa Keyar Dakta Idris Dutsen Tanshi Zuwa Gidan Yari
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    Uwa Ta Mutu A Kokarin Raba Fada Tsakanin ‘Ya’yanta A Abuja
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    ’Yan Fashi Sun Yi Shigar Injiniyoyi, Sun Saci Manyan Na’urorin Sadarwa

MASU ALAKA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota
Kotu Da Ɗansanda

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Next Post
Sin Da Saudiyya Abokai Ne Na Gaskiya Bisa Manyan Tsare-tsare

Sin Da Saudiyya Abokai Ne Na Gaskiya Bisa Manyan Tsare-tsare

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.