ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Rataye Wani Da Ya Yi Wa Budurwa Fyade A Ekiti

by Sabo Ahmad
3 years ago
Fyade

Wata babbar kotun jihar Ekiti, da ke Ado Ekiti ta yanke wa wani mutum mai kimanin shekara 24, mai suna Segun Iwaetan, hukuncin kisa ta hanyar rataya, saboda kama shi da laifin fyaden da ya yi wa wata makociyarsa mai shekara 20, da kuma kama shi da bindiga guda biyu.

An tuhumi wanda ake zargin ne da laifuka guda bakwai wadanda dukkansu ke da alaka da fyade da mallakar bindiga da kuma zama dan kungiyar asiri.

  • Kotu: Mutane 33 Aka Yi Wa Hukunci Daga 11,000 Da Ake Zargin Sun Aikata Fyade A Nijeriya 

Kamar yadda takardar tuhumar ta nuna, “Segun Iwaetan da Atila Iwaetan (wanda a halin yanzu ya gudu), sun hada baki wajen balle gida da sata a shagon Olayemi Oyerinde, suka kwashi kaya wadanda aka kiyasta kudinsu fiye da naira miliyan 1.8.

ADVERTISEMENT

Haka kuma wadanda ake zargin ya yi wa wata mace mai kimanin shekara 20 da ke zaune a Odo Ado, Ado Ekiti fyade, an kuma kama shi da laifin mallakar bindiga guda biyu da kuma laifin zama dan kungiyar asiri.

Wadda aka yi wa fyaden ta ce, “wannan da ya yi min fyadrn makocina ne. A wannan rana da zai yi min fyaden, sai ya shigo dakina da tsakar dare, ina kwance ya tashe ni, ya nuna min bindiga kuma ya ce, idan na yi ihu zai harbe ni. Sai ya ce in cire kayana , a nan ne ya yi min fyade. Bayan ya gama, sai ya roke ni cewa in yafe masa. Ni kuma na ce, na ki.”
Dansanda mai gabatar da kara, Albert Adeyemi, ya gabatar da shaidu guda biyar da suka tabbatar da bayanin wadda aka yi wa fyaden. Lauyan wanda ake zargin, bai kira shaida ko daya ba.

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

Da yake yanke hukunci, mai shari’a Adeniyi Familoni, bayan tabbatar da laifin da ake zargi, ya yanke hukunci kan hada baki wajen aikata laifi da mallakar makami ba bisa ka’ida ba, na shekara 12 a kurkuku, ba tare da zabin tara ba.

“Dangane da batun fyade kuwa, kotun ta yanke hukuncin daurin rai-da-rai,” Sai kuma shiga kungiyar asiri ta Eiye, alkalin ya gaya wa wanda aka gabatar, cewa “hukunci na karshe shi ne na kisa ta hanyar rataya.”

Fyade
Sabo Ahmad
+ postsBio
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    An Gurfanar Da Mutum 3 Bisa Laifin Lakada Wa Wani Duka Har Lahira
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    Dalilin Da Ya Sa Kotu Ta Tasa Keyar Dakta Idris Dutsen Tanshi Zuwa Gidan Yari
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    Uwa Ta Mutu A Kokarin Raba Fada Tsakanin ‘Ya’yanta A Abuja
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    ’Yan Fashi Sun Yi Shigar Injiniyoyi, Sun Saci Manyan Na’urorin Sadarwa

MASU ALAKA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja
Kotu Da Ɗansanda

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

May 2, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

April 25, 2026
An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya

April 25, 2026
Next Post
Sin Da Saudiyya Abokai Ne Na Gaskiya Bisa Manyan Tsare-tsare

Sin Da Saudiyya Abokai Ne Na Gaskiya Bisa Manyan Tsare-tsare

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.