Yau Alhamis, kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin, Guo Jiakun, ya shirya taron manema labarai na yau da kullum da aka saba yi.
Yayin da yake magana dangane da rawar da Sin ta taka a rikicin Iran da Isra’ila, Guo Jiakun ya ce, bayan da rikicin ya barke, shugaba Xi Jinping ya fayyace matsayin kasar Sin kan lamarin, kuma kasar ta ci gaba da mu’amala da kasashen Iran, Isra’ila, Masar, Oman, da sauran bangarori, inda ta yi kira da su dauki matakai cikin gaggawa don sa kaimi ga kwantar da halin da ake ciki yanzu.
- Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
- Ba Za Mu Yarda A Yi Mana Ƙarfa-ƙarfa Ba – Ayatollah Ya Gargaɗi Amurka
Bangaren Sin na son ci gaba da yin hadin gwiwa tare da sauran kasashen duniya don maido da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin Gabas ta Tsakiya cikin sauri.
Bugu da kari, kasar Sin ta yi kira ga bangarorin da rikicin ya shafa musamman Isra’ila, da su sanya moriyar jama’ar kasashen yankin a gaba, da gaggauta tsagaita bude wuta, da sassauta halin da ake ciki yanzu.
Dangane da batun da wasu kafofin yada labarun Amurka suka sanar cewa jami’an Amurka na shirin kai wani hari kan Iran, Guo Jiakun ya ce, Sin na adawa da amfani da karfin tuwo a kan huldar kasa da kasa. Kuma ya kamata kasashen duniya, musamman ma manyan kasashe masu tasiri, su tsaya tsayin daka kan adalci da kuma sauke nauyin dake wuyansu, ta yadda za a samar da yanayi na inganta tsagaita bude wuta da kawo karshen yakin.
Dangane da sanarwar da ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta bayar na cewa za ta maido da yin tambayoyi ga dalibai kafin a ba su biza kuwa, Guo Jiakun ya ce, kasar Sin ta lura da batun, kuma tana fatan Amurka za ta aiwatar da kalaman shugaba Trump na maraba da daliban kasar Sin da su zo Amurka don yin karatu.
Dangane da wani rahoto da wata cibiyar bincike ta kasar Switzerland ta fitar, inda ta bayyana cewa, matsayin karfin yin takara na yankin Hong Kong na Sin ya karu zuwa matsayi na uku a duk fadin duniya, Guo Jiakun ya bayyana cewa, wannan na nuni da matsayin Hong Kong na musamman da kuma alfanun da ake da shi, da kuma tabbatar da ci gaban manufar “Kasa daya, mai tsarin mulki biyu”.(Safiyah Ma)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp