• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Na Taka Rawar Gani A Burinta Na Kaiwa Ga Kololuwar Fitar Da Sinadarin Carbon Nan Zuwa Shekarar 2030

by CMG Hausa
3 years ago
Sin

Yayin da duniya ke fuskantar manyan kalubalolin dake barazana ga rayuwa, da kiwon lafiyar bil adama, daya daga manyan matsalolin da ake fatan shawo kan su shi ne sauyin yanayi.

A bana, kasashe da dama sun fuskanci tsananin zafi dake barazana ga rayuwar al’ummun su, wanda masana da dama ke alakantawa da karuwar dumamar yanayi. Masharhanta da yawa na ganin manyan kasashen duniya sun yi kasa a gwiwa, wajen sauke nauyin dake wuyan su, game da sauya akala daga manfani da nau’o’in makamashi masu dumama yanayi, zuwa sabbin makamashi masu tsafta.

  • Sin Da Indonesiya Za Su Samu Ci Gaba Tare

Sai dai a gefe guda, kasar Sin ta yi nisa wajen aiwatar da manufofinta na dakile dumamar yanayi, inda a baya bayan nan mahukuntan kasar ke cewa, nan da shekarar 2030, kasar za ta kai kololuwar fitar da sinadarin carbon mai dumama yanayi, daga nan kuma adadinsa ya fara raguwa, zuwa yanayin da zai kai ga kawo karshen tasirinsa baki daya.

Ko shakka babu wannan labari ne mai faranta rai, domin kuwa a matsayin ta na kasa mai ci gaban masana’antu, cimma wannan buri zai ba da gagarumar gudummawa, a fannin rage dumamar yanayi a duniya baki daya.

Abun fatan dai shi ne, sauran manyan kasashen duniya, musamman masu ci gaban masana’antu, za su zage damtse wajen sauke nauyin dake wuyan su, a fannin rage tashoshin sarrafa makamashi daga abubuwa masu haifar da dumamar yanayi, su kuma karkata ga amfani da nau’o’in makamashin da ake iya sabuntawa, domin kuwa daukacin bil adama na rayuwa ne cikin wannan duniya kwaya daya, don haka kare muhallin duniya, nauyi ne kan dukkanin al’ummun duniya baki daya. (Saminu Hassan)

LABARAI MASU NASABA

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025
Next Post
Sin: Rahoto Kan Xinjiang Shiri Ne Da Amurka Da Kasashen Yamma Suka Kitsa

Sin: Rahoto Kan Xinjiang Shiri Ne Da Amurka Da Kasashen Yamma Suka Kitsa

LABARAI MASU NASABA

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

November 4, 2025
2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

November 4, 2025
Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

November 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

November 4, 2025
Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

November 4, 2025
Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

November 4, 2025
Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.