ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata A Sake Yi Wa Tsarin Ɗaukar Kuratan Ƴansanda Garanbawul

by Ra'ayinmu
11 months ago
Ƴansanda

Al’umomin a ƙasar nan, na ci gaba da tofa albarkacin bakinsu, kan batun kalubalen rashin tsaro da ke ci gaba da addabar ƙasar. Akasari, an fi yin batun kan yunkurin da jami’an sojin kasar ke ci gaba da yi, na dakile matsalar.

Wannan ya yi daidai da irin gudunmawar da sojin ke bayar wa ne, wajen kare kimar kasar daga dukkan wasu hare-hare, musamman duba da cewa, aikin sojin, ba wai kawai, tabbatar da tsaro, a cikin kasar bane, wajen karfafa doka da oda, a cikin kwayar kasar ba.

Sai dai, a ra’ayin wannan Jaridar, mun lura da irin mahimmancin da sojin suke da shi, wajen karafa tasro a cikin kasar, musamman duba irin, tabarwarewar, lamarin tsaro.

ADVERTISEMENT

Kazalika, wannan kokarin na soji, ba wai kawai, za yi watsi da nauyin da kundin tsarin mulkin kasar, ya dorawa jami’an ƴansanda bane, na gudanar da ayyukan tsaro, a cikin kasar ba.

ɗaukin da soji ke bayar wa wajen tabbatar da tsaro a cikin kasar, ana yi ne, domin kaucewa, take doka da oda, gaba daya.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

  • Dangote Ya Bada Shawarar Samar Da Gidaje Masu Rahusa Da ‘Yan Nijeriya Za Su Iya Mallaka
  • Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana

Sai dai, abin dubi a nan shi ne, yadda kusan yanzu a kasar, tabbatar da doka da oda, a cikin kasar, ya koma kachokam, a huunun sojin.

ɗuba da sashe na 217 na kudin tsarin mulikin Nijeriya na 1999 da aka sabunta, wannan sashen, ayyukan soji tun daga na matakin rundunar sojin kasa da ta ruwa da kuma ta sama shi ne tabbatar da bai wa Nijeriya kariya, daga duk wani nau’in hare-haren, da ka iya zuwa,  daga ketare, musamman ta hanyar, bai wa iyakokin kasar kariya, musamman bayan shugban kasa, ya bayar da umarnin yin hakan, tare da yarjewar, gammaiyyar Majalisun kasar.

Amma a nan, kamar yadda kudin tsarin mulkin kasa ya fayyace, sojin ba su da wani hurumin, maido da  doka da oda, a cikin kwayar kasar.

Sai dai, shugaban kasa na da ikon umartar shigo da soji kan batun dawo da doka oda, domin su taimaka wa ƴansanda.

Wannan kiran na a yiwa tsarin ɗaukar kuratan ƴansandan, za a iya cewa, tsohon batu ne, kusan tun a Jamhuriyya ta hudu ta kasar nan.

Ko da yake dai, wasu gwamnatocin baya, sun yi yunkurin yiwa tsarin garanbawul, sai dai, ba a yi, wani abin azo a gani, kan batun ba.

Misali, tsohowar gwamnatin tsohon shugaban kasa Cif Olusegun Obasanjo a 2006, ta kafa wani kwamati na Fadar shugaban kasa, da ɗan Mandami ya jagoranta, domin a samar da sauye-sauye, a aikin ƴansanda.

Bugu da kari, a lokacin mulkin marigayi tsohon shugaban kasa Umaru Yar’Adua a 2008, ya kafa kwamtin Fadar shugaban kasa, karkashin shugabancin Muhammadu ɗikko Yusuf.

Kazalika, a 2012 tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya kafa kwamtin Fadar shugaban kasa, a karkashin shugabanci Parry Osayande.

A 2018 an kafa kwamitin Fadar shugaban kasa na samar da sauyi kan batun dakarun ƴansanda da ke yakar masu yin fashi da makami wato SARS.

Sai dai, duk irin wannan kokarin da aka yi a baya, matsalar ba sake Zane ba

A nan muna nuna damuwarmu, kan rashin samar da tsarin da ya dace, na yin sauye-sauye a aikin na ƴasanda.

Ra’ayin wannan Jaridar, ya zo daidai da cewa, batu daya da ke kawo cikas kan samar da ingantaccen tsari a aikin na ƴansanda shi ne, na rashin kyakyawan ɗaukar jami’an aikin.

ɗukkan irin sauye-sauyen da za a samar na ɗaukar kuratan, zai yi wuya a cimma wata nasarar kirki, matukar tsarin na ɗaukar kuratan, ya ci gaba da zama, ana yinsa, ba bisa ka’ida ba.

Batun ɗaukar kuratan ba abu ne na was aba, dole ne rinka ɗaukar kuratan, masu halayya ta gari ba masu kashi a gindi ba.

Idan za a iya tunawa, a 2024, an tayar da Jijiyar Wuya a tsakanin rundunar ƴansanda ta kasa da Hukumar kula da aikin ƴan sanda na kasa, kan batun ɗaukar kurata sama oɓer 10,000 da kuma ɗaukar, kurata na musamman.

An ruwaito Kakakin runudanar ƴansanda na kasa ACP Olumuyiwa Adejobi, ya shelanta cewa, ɗaukar wadanan kuratan na cike da kura-kurai da dama da aka tabka, ciki har da na zargin cin hanci, har da kuma sanya sunayen wasu, da ma ba su nemi shiga aikin ba, wasun kuma, ba su iya tsallake gwaje-gwajen da aka yi masu na kiwon lafiyarsu ba.

Hakazalika, a 2022 a lokacin mulkin toshon shugaban kasa marigayi Muhammadu Buhari, gwamnatinsa ta kirkiro da sabon tsari ga aikin, musamman domin a tabbatar da an inganta aiki yadda zai iya yakar duk wani nau’I, na aikata manyan laifuka da kare rayukan yan Nijeriya da kuma dukiyoyinsu a karkashin doka ta  2020.

Sai dai, duk da hakan, wannan manufar, hakar bata cimma ruwa ba, musamman kan batun ɗaukar ingantattun kuratan.

Kazalika, a kwanan baya, Ma’aikatar Kula da Jindadi da Walwalar ƴansanda tare da hadaka da rundunar ƴansanda ta kasa, ta kaddamar da  kudurin farfado da aikin ƴansanda.

Sai dai, Ma’aikatar a cikin wannan kudirin, ba ta tabo batun tsarin yin garanbawul kan ɗaukar kuratan ba.

Ko da yake dai, wannan Jaridar ta jinjinawa wannan kokarin na mahukuntan ƴansandan da suka yi a baya, amma Jaridar, na da ra;ayin cewa, dole ne a samar da kyakyawan tsari na ɗaukar kuratan ƴansandan, musamman a tabbatar da ba dauki wadanda ke wani guntun kashi, na aikata laifi ba. Yin hakan shi ne, babban ginshiki kuma madogararmu, a nan.

Ƴansanda
Ra'ayinmu
+ postsBio
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Ce-ce-ku-ce Kan Batun Biyan Bashin Naira Tiriliyan 3.3 Na Kuɗin Lantarki
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Matsalar Ɓacewar Gandun Dazukan Nijeriya

MASU ALAKA

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Maniyyatan Nijeriya
Manyan Labarai

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
'Yan Bindiga
Manyan Labarai

Yan Bindiga Sun Kashe Manoma Shida A Birnin Gwari Ta Jihar Kaduna

June 23, 2026
Next Post
Taɓarɓarewar Tarbiyyar Matasa A Arewa: Ƙalubalen Da Ke Gaban Iyaye Da Shugabanni

Taɓarɓarewar Tarbiyyar Matasa A Arewa: Ƙalubalen Da Ke Gaban Iyaye Da Shugabanni

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.