• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Ta Baiwa Duk Duniya Sako Mai Yakini

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Ta Baiwa Duk Duniya Sako Mai Yakini
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS, kana ministan harkokin wajen kasar Wang Yi, ya amsa tambayoyin da ’yan jarida na gida da waje suka yi masa, a gun taron manema labarai da aka gudanar kan manyan taruka biyu wato na NPC da CPPCC, wadanda suka shafi huldar kasa da kasa da abubuwa masu jan hankalin mutane da daidaita harkokin duniya da sauransu. Amsoshin da ministan ya bayar dangane da tambayoyin da aka yi masa, sun baiwa duk fadin duniya sako mai yakini cewa, Sin tana taka rawar gani a duniya bisa bunkasuwarta mai karko.

“Sin za ta nace ga matsayin kasancewar karfi mai karko wajen ciyar da zaman lafiya da ci gaban duniya gaba”, kafofin yada labarai na kasa da kasa sun mai da wannan magana matsayin da Sin take dauka ta fuskar diplomasiyya.

  • Ba Za Mu Lamunci Cin Zarafin Wani Da Sunan Tafsiri Ba – Gwamnatin Kaduna
  • Wasoso Da Fasa Rumbunan Hatsi Ba Za Su Magance Yunwa Ba – Farfesa Sanda

A halin yanzu, ana ci gaba da fama da rikicin Ukraine, baya ga rikicin Palasdinu da Isar’ila dake kara tsananta, kuma siyasar yankuna na kara kamari. Ba fatan tabbatar da tsaro da zaman lafiya cikin kasarta kadai Sin ke yi ba, har ma da son taka rawa wajen samar da zaman lafiya a duk duniya

A gun taron manema labarai, Sin ta gabatar da wata hanya mai salon kasar wajen magance matsalolin dake jan hankalin mutane, wato nacewa ga hana tsoma baki cikin harkokin gidan sauran kasashe, da warware rikici a siyasance bisa adalci da daidaito, ta yadda za a daidaita batutuwa daga tushe.

Manufar da Sin take dauka wajen magance harkokin duniya ita ce, gudanar da harkokin duniya tsakanin bangarori daban-daban cikin adalci bisa oda da doka, da samun ci gaban tattalin arzikin duniya tare bisa ka’idar hakuri da juna, matakin da ya dace da halin da ake ciki, kuma ya bayyana muradun kasashe masu tasowa baki daya.

Labarai Masu Nasaba

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kazalika, duniya na fama da karancin karfin samun bunkasuwa, kana wasu kasashe na daukar matakin katse hulda, game da hakan, Sin ta bayyana matsayin da ta kan dauka cewa, dole ne a kafa tsarin tattalin arziki mai bude kofa.

Bugu da kari, a shekarar bara, yawan bunkasuwar Sin ya kai kashi 5.2%, wanda ya taka rawa na kashi 1/3 ga bunkasuwar tattalin arzikin duniya, hakan ya sa Sin take taka rawar gani wajen ingiza bunkasuwar duniya.

Yanzu, duniya na shiga wani yanayi mai cike da mabambantan sauye-sauye, jama’ar duniya na ganin muhimmancin kafa kyakkyawar makomar Bil Adama ta bai daya, da fahimtar rawa mai dorewa da Sin take bayarwa. A lokacin bazarar bana, wadannan manyan taruka biyu na fitar da sako mai yakini ga duk fadin duniya cewa, Sin za ta ci gaba da ingiza bunkasuwar duniya mai dorewa ba tare da sauyawa ba. (Amina Xu)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Za Mu Lamunci Cin Zarafin Wani Da Sunan Tafsiri Ba – Gwamnatin Kaduna

Next Post

Kasar Sin Ta Gano Filin Hakar Mai Na Farko A Ruwa Mai Zurfi Mai Yawan Ton Miliyan 100

Related

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

2 hours ago
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

2 hours ago
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II
Daga Birnin Sin

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

3 hours ago
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO
Daga Birnin Sin

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

5 hours ago
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”
Daga Birnin Sin

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

6 hours ago
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi
Daga Birnin Sin

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

8 hours ago
Next Post
Kasar sin

Kasar Sin Ta Gano Filin Hakar Mai Na Farko A Ruwa Mai Zurfi Mai Yawan Ton Miliyan 100

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.