ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Ta Baiwa Duk Duniya Sako Mai Yakini

by CGTN Hausa
3 years ago
Sin

Mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS, kana ministan harkokin wajen kasar Wang Yi, ya amsa tambayoyin da ’yan jarida na gida da waje suka yi masa, a gun taron manema labarai da aka gudanar kan manyan taruka biyu wato na NPC da CPPCC, wadanda suka shafi huldar kasa da kasa da abubuwa masu jan hankalin mutane da daidaita harkokin duniya da sauransu. Amsoshin da ministan ya bayar dangane da tambayoyin da aka yi masa, sun baiwa duk fadin duniya sako mai yakini cewa, Sin tana taka rawar gani a duniya bisa bunkasuwarta mai karko.

“Sin za ta nace ga matsayin kasancewar karfi mai karko wajen ciyar da zaman lafiya da ci gaban duniya gaba”, kafofin yada labarai na kasa da kasa sun mai da wannan magana matsayin da Sin take dauka ta fuskar diplomasiyya.

  • Ba Za Mu Lamunci Cin Zarafin Wani Da Sunan Tafsiri Ba – Gwamnatin Kaduna
  • Wasoso Da Fasa Rumbunan Hatsi Ba Za Su Magance Yunwa Ba – Farfesa Sanda

A halin yanzu, ana ci gaba da fama da rikicin Ukraine, baya ga rikicin Palasdinu da Isar’ila dake kara tsananta, kuma siyasar yankuna na kara kamari. Ba fatan tabbatar da tsaro da zaman lafiya cikin kasarta kadai Sin ke yi ba, har ma da son taka rawa wajen samar da zaman lafiya a duk duniya

ADVERTISEMENT

A gun taron manema labarai, Sin ta gabatar da wata hanya mai salon kasar wajen magance matsalolin dake jan hankalin mutane, wato nacewa ga hana tsoma baki cikin harkokin gidan sauran kasashe, da warware rikici a siyasance bisa adalci da daidaito, ta yadda za a daidaita batutuwa daga tushe.

Manufar da Sin take dauka wajen magance harkokin duniya ita ce, gudanar da harkokin duniya tsakanin bangarori daban-daban cikin adalci bisa oda da doka, da samun ci gaban tattalin arzikin duniya tare bisa ka’idar hakuri da juna, matakin da ya dace da halin da ake ciki, kuma ya bayyana muradun kasashe masu tasowa baki daya.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Kazalika, duniya na fama da karancin karfin samun bunkasuwa, kana wasu kasashe na daukar matakin katse hulda, game da hakan, Sin ta bayyana matsayin da ta kan dauka cewa, dole ne a kafa tsarin tattalin arziki mai bude kofa.

Bugu da kari, a shekarar bara, yawan bunkasuwar Sin ya kai kashi 5.2%, wanda ya taka rawa na kashi 1/3 ga bunkasuwar tattalin arzikin duniya, hakan ya sa Sin take taka rawar gani wajen ingiza bunkasuwar duniya.

Yanzu, duniya na shiga wani yanayi mai cike da mabambantan sauye-sauye, jama’ar duniya na ganin muhimmancin kafa kyakkyawar makomar Bil Adama ta bai daya, da fahimtar rawa mai dorewa da Sin take bayarwa. A lokacin bazarar bana, wadannan manyan taruka biyu na fitar da sako mai yakini ga duk fadin duniya cewa, Sin za ta ci gaba da ingiza bunkasuwar duniya mai dorewa ba tare da sauyawa ba. (Amina Xu)

 

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Kasar sin

Kasar Sin Ta Gano Filin Hakar Mai Na Farko A Ruwa Mai Zurfi Mai Yawan Ton Miliyan 100

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.