A yau Juma’a ma’aikatar tsaron kasar Sin, ta yi kira ga kasar Philippines da ta kaucewa yin kasada, ta kuma dakatar da duk wasu matakai na keta hakki, da tada zaune tsaye a tekun kudancin Sin.
Da yake bayyana kiran yayin taron manema labarai na rana-rana da ya gudana a yau, kakakin ma’aikatar Zhang Xiaogang, ya ce “Sojojin kasar Sin ba ma fatan ganin tashin wata tarzoma, amma idan fada ya zo, ba za mu ja da baya ba.”
- Xi Ya Jaddada Muhimmancin Kyautata Tsarin Yawon Bude Ido Na Zamani
- Ziyarar Xi Jinping A Turai Ta Fitar Da Muryar Kiyaye Zaman Lafiya Da Yin Hadin Gwiwa
Zhang ya kara da cewa, Sin ta sha alwashin ci gaba da aiwatar da kwararan matakai na kare mulkin kai na yankunanta, da hakkoki da moriyar yankunan teku, da kare zaman lafiya da daidaito a yankin tekun kudancin kasar.
Ya ce, game da batun tekun kudancin Sin, wane ne ke furta wani abu ya kuma aikata sabaninsa? Wane ne yake dagewa wajen tada zaune tsaye, da haifar da tashin tashina? Kuma wane ne ke ingiza yanayin zaman dar-dar da janyo fito-na-fito, da kara lalata yanayin da ake ciki a yankin na tekun kudancin Sin? Ko shakka babu duniya na kallon wadannan abubuwa a zahiri. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp