ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zanga-zangar Karin Kudin Wuta: Gwamnati Ta Shelanta Matakin Da Za Ta Dauka

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Wuta

Biyo bayan tirjiya na karin kudin wutan lantarki da hukumomi suka yi a Nijeriya a watan da ta gabata, kungiyar kwadago a Nijeriya sun dukufa wajen gudanar da zanga-zanga tare da neman dole a canye zancen karin kudin wuta da kuma magance matsalar wutar lantarki.

Rahotonni sun yi nuni da cewa kungiyar kwadago sun rufe dukkanin ofisoshin kamfanonin rarraba wutar lantaki guda 11 da babban ofishin hukumar kula da wutar lantarki ta kasa a yayin da suka tsunduma gudanar da zanga-zangar na ranar Litinin.

  • Sin: Karbuwar Hajojin Sin Masu Nasaba Da Sabbin Makamashi Ba Shi Da Nasaba Da Samar Da Tallafi
  • Za A Bude Shafin Karbar Bashin Dalibai A Ranar 24 Ga Mayu

Shugaban kungiyar kwadago, Joe Ajaero shi ne ya jagoranci zanga-zangar a Abuja har zuwa ga ministan wuta da kuma shalkwatar hukumar kula da lamarin wuta a Nijeriya (NERC).

ADVERTISEMENT

 Sannan an rufe ofishin kamfanin rarraba wutar lantarki tare da hana ma’aikata shiga domin gudanar da aiki.

 Bugu da kari, haka zancen yake a sauran ofisoshin kamfanin da ke jihohi da suka hada da na Kwara, Legas, Kaduna, Filato, Inugu, Sakkwato, Bauchi da sauran ofisoshi da suke sassan kasar nan.

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Ajaero, yayin zanga-zangar, ya ce akwai bukatar NERC ta sake nazarin matakan da suka bi wajen karin kudin wuta. Ya ce, karin kudin ya janyo tashin farashin ababe da dama musamman kayan abinci.

 A martaninta kan zanga-zangar na kwana guda, gwamnatin Nijeriya ta ce ta fara tattaunawa da kungiyar kwadago kan lamarin.

Kakakin ministan wuta a Nijeriya, Florence Eke, ta shaida wa majiyarmu ta wayar tarho cewa bayan zanga-zangar ma’aikatan, gwamnatin tarayya ta hannun babban sakatare, Mista Mamman Mahmuda, ya kira taron ganawa da kungiyar kwadago a mako mai zuwa, ganawar da zai hada har da masu ruwa da tsaki domin lalubo bakin zaren matsalar.

“Ma’aikatar wuta za ta gayyaci dukkanin masu ruwa da tsaki domin nemo mafita kan wannan batun a mako mai zuwa,” ta shaida.

Mai magana da yawun kungiyar kwadago, Benson Upah, ya ce, ya kamata ne gwamnati ta tuntubi masu ruwa da tsaki tun kafin ta aiwatar da manufar karin kudin wutar a ranar 3 ga watan Afrilu.

Ya tabbatar da cewa zanga-zanga da suka fara muddin gwamnati ta kasa komawa baya kan matakinta na karin kudin lantarki za su ci gaba.

Idan za a tuna dai a watan Afrilun 2024 ne hukumar kula da wutar lantarki a Nijeriya ta sanar da karin kudin lantarki da kaso 240 ga kwastomomin da ke amfani da rukunin A.

Wuta
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Next Post
Yadda Sin Da Rasha Suke Mu’amala Da Juna Ya Samar Da Kwanciyar Hankali A Duniya

Yadda Sin Da Rasha Suke Mu’amala Da Juna Ya Samar Da Kwanciyar Hankali A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.