• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Ta Ciri Tuta A Fannin Ingiza Koyi Da Juna Tsakanin Mabanbantan Wayewar Kai

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Ta Ciri Tuta A Fannin Ingiza Koyi Da Juna Tsakanin Mabanbantan Wayewar Kai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A cikin jawabin da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar na maraba da sabuwar shekarar nan ta 2025, ya jaddada aniyar kasarsa ta ci gaba da aiki tare da sauran kasashen duniya, don kara inganta koyi da juna tsakanin mabanbantan aladu da wayewar kai. Wadannan kalamai na shugaba Xi, shaida ce dake kara fito da shirin kasar Sin fili, a fannin amfani da kwarewa, da hangen nesa wajen ingiza kyakkyawan yanayin zaman tare tsakanin wayewar kai daban daban, da ma kwazon kasar na sauke nauyin dake wuyanta, na yayata ci gaban wayewar kan daukacin bil adama.

Ko shakka babu duniyar yau tana cike da sabbin yanayi na tangal-tangal, da sauye-sauye, yayin da karin kalubale ke bullowar duniya. Kuma magance manyan kalubalen dake addabar dan adam na bukatar wanzar da zaman lafiya, da zaman jiyuwa tsakanin mabanbantan wayewar kai.

  • Xi Ya Jagoranci Taron Shugabannin JKS Game Da Ayyukan Tallafin Jin Kai Bayan Aukuwar Girgizar Kasa A Xizang
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Ya Lashi Takobin Karfafa Hadin Gwiwa Da Afirka

A gani na, yayin da wasu sassan kasa da kasa ke aiwatar da matakan ware kai, da baiwa kasuwa kariya, da nuna fifiko, kasar Sin a nata bangare ta rungumi matakai masu kyau na sada zumunta da sauran sassa, ta hanyar musaya, da koyi da juna, matakan da za su baiwa sassan kasa da kasa damar amfana daga wayewar kan kasar Sin, wanda ya samo asali daga tarihinta na sama da shekaru 5,000.

Sanin kowa ne cewa cin gajiyar wayewar kai, da bunkasa rayuwar dan adam ba za su samu ba, muddin ba a cimma matsaya, da budewa juna kofa, da yin tafiya tare, da musaya, da koyi da juna tsakanin mabambantan wayewar kai ba. Kara tattaunawa zai rage fito na fito, yayin da yin tafiya tare zai rage rashin fahimtar juna. Hakan ne ma ya sa a watan Yunin shekarar 2024 da ta gabata, babban taron MDD karo na 78, da babban rinjaye ya amince da kudurin da kasar Sin ta gabatar, na kafa ranar kasa da kasa ta tattaunawa tsakanin mabanbantan wayewar kai. Wani mataki da a gani na ya zama misali, na yadda kasar ta Sin ke gabatarwa duniya dabarun warware wasu manyan matsaloli, musamman a wannan gaba da nufin kawar da kyamar juna, da ingiza fahimtar juna, da kyautata amincewa juna tsakanin sassan kasa da kasa.

A daya bangaren kuma, cimma burin zamanantarwa muhimmin batu ne mai nasaba da fatan bunkasa wayewar kan dan adam. Zamanantarwa ba aiki ne da ya shafi wasu tsirarun kasashe kalilan ba, kana ba zai yiwu ya zamo salo daya tak da za a kwafa daga wani yanki a kai wani yanki ba. A tafiyar zamanantarwa, kasar Sin ta yi imani da yin tafiya, da aiki tare da sauran kasashe, ta yadda za su hada karfi da karfe wajen yin musayar kwarewa, har a kai ga gina kasashe daban daban, da gina alummar duniya mai kyakkyawar makomar bai daya, wadda daukacin bil adama zai yi alfahari da ita.(Saminu Alhassan)

Labarai Masu Nasaba

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Jagoranci Taron Shugabannin JKS Game Da Ayyukan Tallafin Jin Kai Bayan Aukuwar Girgizar Kasa A Xizang

Next Post

Everton Ta Sallami Kocinta, Sean Dyche

Related

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani
Daga Birnin Sin

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

35 minutes ago
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya
Daga Birnin Sin

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

20 hours ago
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

21 hours ago
An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

22 hours ago
Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

23 hours ago
Sin Ta Yi Kira Da A Ci Gaba Da Himmatuwa Wajen Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Ci Gaba Da Himmatuwa Wajen Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

24 hours ago
Next Post
Everton Ta Sallami Kocinta, Sean Dyche

Everton Ta Sallami Kocinta, Sean Dyche

LABARAI MASU NASABA

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

July 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

July 27, 2025
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.