• English
  • Business News
Tuesday, October 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Ta Ciri Tuta A Fannin Ingiza Koyi Da Juna Tsakanin Mabanbantan Wayewar Kai

byCGTN Hausa and Sulaiman
9 months ago
inDaga Birnin Sin
0
Sin Ta Ciri Tuta A Fannin Ingiza Koyi Da Juna Tsakanin Mabanbantan Wayewar Kai

A cikin jawabin da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar na maraba da sabuwar shekarar nan ta 2025, ya jaddada aniyar kasarsa ta ci gaba da aiki tare da sauran kasashen duniya, don kara inganta koyi da juna tsakanin mabanbantan aladu da wayewar kai. Wadannan kalamai na shugaba Xi, shaida ce dake kara fito da shirin kasar Sin fili, a fannin amfani da kwarewa, da hangen nesa wajen ingiza kyakkyawan yanayin zaman tare tsakanin wayewar kai daban daban, da ma kwazon kasar na sauke nauyin dake wuyanta, na yayata ci gaban wayewar kan daukacin bil adama.

Ko shakka babu duniyar yau tana cike da sabbin yanayi na tangal-tangal, da sauye-sauye, yayin da karin kalubale ke bullowar duniya. Kuma magance manyan kalubalen dake addabar dan adam na bukatar wanzar da zaman lafiya, da zaman jiyuwa tsakanin mabanbantan wayewar kai.

  • Xi Ya Jagoranci Taron Shugabannin JKS Game Da Ayyukan Tallafin Jin Kai Bayan Aukuwar Girgizar Kasa A Xizang
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Ya Lashi Takobin Karfafa Hadin Gwiwa Da Afirka

A gani na, yayin da wasu sassan kasa da kasa ke aiwatar da matakan ware kai, da baiwa kasuwa kariya, da nuna fifiko, kasar Sin a nata bangare ta rungumi matakai masu kyau na sada zumunta da sauran sassa, ta hanyar musaya, da koyi da juna, matakan da za su baiwa sassan kasa da kasa damar amfana daga wayewar kan kasar Sin, wanda ya samo asali daga tarihinta na sama da shekaru 5,000.

Sanin kowa ne cewa cin gajiyar wayewar kai, da bunkasa rayuwar dan adam ba za su samu ba, muddin ba a cimma matsaya, da budewa juna kofa, da yin tafiya tare, da musaya, da koyi da juna tsakanin mabambantan wayewar kai ba. Kara tattaunawa zai rage fito na fito, yayin da yin tafiya tare zai rage rashin fahimtar juna. Hakan ne ma ya sa a watan Yunin shekarar 2024 da ta gabata, babban taron MDD karo na 78, da babban rinjaye ya amince da kudurin da kasar Sin ta gabatar, na kafa ranar kasa da kasa ta tattaunawa tsakanin mabanbantan wayewar kai. Wani mataki da a gani na ya zama misali, na yadda kasar ta Sin ke gabatarwa duniya dabarun warware wasu manyan matsaloli, musamman a wannan gaba da nufin kawar da kyamar juna, da ingiza fahimtar juna, da kyautata amincewa juna tsakanin sassan kasa da kasa.

A daya bangaren kuma, cimma burin zamanantarwa muhimmin batu ne mai nasaba da fatan bunkasa wayewar kan dan adam. Zamanantarwa ba aiki ne da ya shafi wasu tsirarun kasashe kalilan ba, kana ba zai yiwu ya zamo salo daya tak da za a kwafa daga wani yanki a kai wani yanki ba. A tafiyar zamanantarwa, kasar Sin ta yi imani da yin tafiya, da aiki tare da sauran kasashe, ta yadda za su hada karfi da karfe wajen yin musayar kwarewa, har a kai ga gina kasashe daban daban, da gina alummar duniya mai kyakkyawar makomar bai daya, wadda daukacin bil adama zai yi alfahari da ita.(Saminu Alhassan)

Labarai Masu Nasaba

Habakar Yin Sayayya A Lokacin Hutu Ta Nuna Kirkira Da Irin Ci Gaban Da Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samu   

Karamin Ofishin Jakadancin Sin Da Ke Legas Ya Yi Bikin Bunkasa Al’adu Na Bikin Tsakiyar Kaka

ShareTweetSendShare
CGTN Hausa and Sulaiman

CGTN Hausa and Sulaiman

Related

Habakar Yin Sayayya A Lokacin Hutu Ta Nuna Kirkira Da Irin Ci Gaban Da Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samu   
Daga Birnin Sin

Habakar Yin Sayayya A Lokacin Hutu Ta Nuna Kirkira Da Irin Ci Gaban Da Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samu   

20 hours ago
Karamin Ofishin Jakadancin Sin Da Ke Legas Ya Yi Bikin Bunkasa Al’adu Na Bikin Tsakiyar Kaka
Daga Birnin Sin

Karamin Ofishin Jakadancin Sin Da Ke Legas Ya Yi Bikin Bunkasa Al’adu Na Bikin Tsakiyar Kaka

21 hours ago
Nazari Ya Gano Falalen Dutse Na Yanki Mai Nisa A Duniyar Wata Ya Fi Tsananin Sanyi Fiye Da Na Yanki Na Kusa
Daga Birnin Sin

Nazari Ya Gano Falalen Dutse Na Yanki Mai Nisa A Duniyar Wata Ya Fi Tsananin Sanyi Fiye Da Na Yanki Na Kusa

22 hours ago
Next Post
Everton Ta Sallami Kocinta, Sean Dyche

Everton Ta Sallami Kocinta, Sean Dyche

LABARAI MASU NASABA

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane

October 7, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

October 7, 2025
Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

October 7, 2025
Tsaro: Gwamnan Kogi Ya Ayyana Yaƙi Da Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ka’ida Ba Da ‘Yan Bindiga

Tsaro: Gwamnan Kogi Ya Ayyana Yaƙi Da Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ka’ida Ba Da ‘Yan Bindiga

October 7, 2025
Majalisar Wakilai Ta Kafa Kwamiti Da Zai Binciki Harkokin Kirifto Da POS A Nijeriya

Majalisar Wakilai Ta Kafa Kwamiti Da Zai Binciki Harkokin Kirifto Da POS A Nijeriya

October 7, 2025
Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa

Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa

October 7, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Rage Kuɗin Aikin Hajjin 2026

October 7, 2025
Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano

Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano

October 6, 2025
Kada Ku Yi Sanadiyar Rugujewar Matatar Mai Ta Dangote – Shettima Ga PENGASSAN 

Kada Ku Yi Sanadiyar Rugujewar Matatar Mai Ta Dangote – Shettima Ga PENGASSAN 

October 6, 2025
Habakar Yin Sayayya A Lokacin Hutu Ta Nuna Kirkira Da Irin Ci Gaban Da Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samu   

Habakar Yin Sayayya A Lokacin Hutu Ta Nuna Kirkira Da Irin Ci Gaban Da Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samu   

October 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.