• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Ta Jagoranci Kaddamar Da Shirin Aiwatar Da “Tsarin Kunming-Montreal” A Taron Sauyin Yanayi Na MDD A Hukumance

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Ta Jagoranci Kaddamar Da Shirin Aiwatar Da “Tsarin Kunming-Montreal” A Taron Sauyin Yanayi Na MDD A Hukumance
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar 9 ga wata bisa agogon wurin, yayin biki mai taken “Natural Day” na babban taron kasashen da suka rattaba hannu kan yarjejeniyar sauyin yanayi ta MDD karo 28 COP28 da ake gudanar a birnin Dubai na hadaddiyar daular Larabawa, kasar Sin ta sanar da shiga kungiyar “ High Ambition Alliance for Nature and Humanity” a hukumance, inda ta jagoranci kaddamar da shirin aiki na “Kunming-Montreal Global Diversity Framework”.

A yayin bikin, shugaban babban taron sassan da suka amince da yarjejeniyar kare mabambantan halittu karo na 15, kuma ministan kula da muhalli na kasar Sin, Huang Runqiu ya bayyana ta kafar bidiyo cewa, matsalar sauyin yanayi da yadda ake asarar mabambantan halittu, suna haifar da babban kalubale ga rayuwa da ma ci gaban bil-Adama. Kasar Sin na fatan babban taron na COP28, zai aiwatar da hadin gwiwa tsakanin bangarori da dama bisa gaskiya, tare da samun sakamako mai kyau da kuma inganci.

  • Hangzhou: An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Kan Shirye-shiryen Rediyo Da Telebijin Karo Na 6
  • Sin Ta Bayyana Matukar Adawa Da Kin Amincewar Amurka Da Kudurin Tsagaita Wuta Domin Jin Kai

Huang Runqiu ya kuma yi kira ga dukkan bangarorin da su gaggauta yin kwaskwarima ga “manyan tsare-tsare da shirin ayyukan kiyaye mabambantan halittu”, da kuma tattara karin albarkatu, don kara azama kan cimma manyan manufofi guda uku na yarjejeniyar kare mabambantan halittu bisa daidaito.

Kasar Sin tana maraba da dukkan masu ruwa da tsaki, da su taka rawar gani wajen gudanar da harkokin kula da mabambantan halittu, kuma tana matukar yabawa da goyon bayan dukkan alkawura da tsare-tsare da hadin gwiwar da suka dace, wajen sa kaimi ga aiwatar da tsarin aikin Kunming-Montreal.

Kasar Sin tana son yin hadin gwiwa tare da kasashen duniya, wajen tinkarar kalubalen da duniya ke fuskanta kamar hasarar rabe-raben halittu da matsalar sauyin yanayi, tare da sa kaimi ga cimma nasarar gudanar da babban taron bangarorin da suka rattaba hannu kan yarjejeniyar sauyin yanayi ta MDD karo na 28 COP28, domin samar da duniya mai kyau inda za a samu zaman jituwa tsakanin mutum da yanayi.

Labarai Masu Nasaba

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sannan, a yayin taron manema labaru na farko da tawagar kasar Sin mai halartar babban taron kasashen duniya da suka sanya hannu kan yarjejeniyar MDD kan sauyin yanayi karo na 28 COP28 ta gudanar a jiya, manzon musamman mai kula da harkokin sauyin yanayi na kasar Sin Xie Zhenhua ya yi bayani game da nasarorin da Sin ta samu wajen canja tsarin raya kasa tare da kiyaye muhalli da raya makamashin da za a iya sabuntawa. Xie ya ce, kasar Sin za ta ci gaba da yin hadin gwiwa tare da kasa da kasa wajen tinkarar sauyin yanayi.

Xie Zhenhua ya bayyana cewa, kasar Sin ta samar da babbar gudummawa wajen kyautata tsarin samar da makamashi da raya makamashin da za a iya sabuntawa. Ya zuwa yanzu, yawan kudin da aka kashe wajen samar da wutar lantarki ta hanyar amfani da karfin iska ya ragu da kashi 80 cikin dari, yawansu ta hanyar hasken rana ya ragu da kashi 90 cikin dari, wadanda suka aza tubalin yin amfani da irin wannan makamashi a fadin duniya. A halin yanzu, yawan na’urorin samar da makamashin da za a sabuntawa ya fi yawan na kwal, wannan wani babban canji ne a tsarin samar da makamashi. Sin za ta ci gaba da yin amfani da makamashin da za a iya sabuntawa don maye gurbin makamashin kwal da sauran burbushin halittu.

Wakilin Sin ya kara da cewa, Sin ta hada kai da kasashe da yankuna fiye da 100, kan ayyukan samar da makamashi masu tsabta, da daddale yarjejeniyoyin fahimtar juna kan hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa wajen tinkarar sauyin yanayi tare da kasashe masu tasowa fiye da 10. A nan gaba Sin za ta ci gaba da yin hadin gwiwa tare da kasashe masu tasowa don inganta hadin gwiwarsu a fannonin kudi da fasahohi. (Ibrahim Yaya, Zainab Zhang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yawan Yaran Da Ke Fama Da Cututtuka Masu Alaka Da Sassan Jiki Masu Taimakawa Numfashi Ya Ragu A Kasar Sin

Next Post

Na Samu Farin Ciki Sosai A Farkon Fara Rubutuna – Fauziyya

Related

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa
Daga Birnin Sin

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

17 hours ago
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

18 hours ago
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

19 hours ago
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci
Daga Birnin Sin

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

20 hours ago
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu
Daga Birnin Sin

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

22 hours ago
Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo
Daga Birnin Sin

Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

2 days ago
Next Post
Na Samu Farin Ciki Sosai A Farkon Fara Rubutuna – Fauziyya

Na Samu Farin Ciki Sosai A Farkon Fara Rubutuna - Fauziyya

LABARAI MASU NASABA

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

October 5, 2025
Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.