ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Ta Jagoranci Kaddamar Da Shirin Aiwatar Da “Tsarin Kunming-Montreal” A Taron Sauyin Yanayi Na MDD A Hukumance

by CGTN Hausa
2 years ago
MDD

A ranar 9 ga wata bisa agogon wurin, yayin biki mai taken “Natural Day” na babban taron kasashen da suka rattaba hannu kan yarjejeniyar sauyin yanayi ta MDD karo 28 COP28 da ake gudanar a birnin Dubai na hadaddiyar daular Larabawa, kasar Sin ta sanar da shiga kungiyar “ High Ambition Alliance for Nature and Humanity” a hukumance, inda ta jagoranci kaddamar da shirin aiki na “Kunming-Montreal Global Diversity Framework”.

A yayin bikin, shugaban babban taron sassan da suka amince da yarjejeniyar kare mabambantan halittu karo na 15, kuma ministan kula da muhalli na kasar Sin, Huang Runqiu ya bayyana ta kafar bidiyo cewa, matsalar sauyin yanayi da yadda ake asarar mabambantan halittu, suna haifar da babban kalubale ga rayuwa da ma ci gaban bil-Adama. Kasar Sin na fatan babban taron na COP28, zai aiwatar da hadin gwiwa tsakanin bangarori da dama bisa gaskiya, tare da samun sakamako mai kyau da kuma inganci.

  • Hangzhou: An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Kan Shirye-shiryen Rediyo Da Telebijin Karo Na 6
  • Sin Ta Bayyana Matukar Adawa Da Kin Amincewar Amurka Da Kudurin Tsagaita Wuta Domin Jin Kai

Huang Runqiu ya kuma yi kira ga dukkan bangarorin da su gaggauta yin kwaskwarima ga “manyan tsare-tsare da shirin ayyukan kiyaye mabambantan halittu”, da kuma tattara karin albarkatu, don kara azama kan cimma manyan manufofi guda uku na yarjejeniyar kare mabambantan halittu bisa daidaito.

ADVERTISEMENT

Kasar Sin tana maraba da dukkan masu ruwa da tsaki, da su taka rawar gani wajen gudanar da harkokin kula da mabambantan halittu, kuma tana matukar yabawa da goyon bayan dukkan alkawura da tsare-tsare da hadin gwiwar da suka dace, wajen sa kaimi ga aiwatar da tsarin aikin Kunming-Montreal.

Kasar Sin tana son yin hadin gwiwa tare da kasashen duniya, wajen tinkarar kalubalen da duniya ke fuskanta kamar hasarar rabe-raben halittu da matsalar sauyin yanayi, tare da sa kaimi ga cimma nasarar gudanar da babban taron bangarorin da suka rattaba hannu kan yarjejeniyar sauyin yanayi ta MDD karo na 28 COP28, domin samar da duniya mai kyau inda za a samu zaman jituwa tsakanin mutum da yanayi.

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Koriya Ta Arewa Na Fuskantar Sabbin Damammaki Da Kudurori In Ji Shugaba Xi Jinping

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga EU Ta Hada Hannu Da Ita Domin Inganta Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakaninsu

Sannan, a yayin taron manema labaru na farko da tawagar kasar Sin mai halartar babban taron kasashen duniya da suka sanya hannu kan yarjejeniyar MDD kan sauyin yanayi karo na 28 COP28 ta gudanar a jiya, manzon musamman mai kula da harkokin sauyin yanayi na kasar Sin Xie Zhenhua ya yi bayani game da nasarorin da Sin ta samu wajen canja tsarin raya kasa tare da kiyaye muhalli da raya makamashin da za a iya sabuntawa. Xie ya ce, kasar Sin za ta ci gaba da yin hadin gwiwa tare da kasa da kasa wajen tinkarar sauyin yanayi.

Xie Zhenhua ya bayyana cewa, kasar Sin ta samar da babbar gudummawa wajen kyautata tsarin samar da makamashi da raya makamashin da za a iya sabuntawa. Ya zuwa yanzu, yawan kudin da aka kashe wajen samar da wutar lantarki ta hanyar amfani da karfin iska ya ragu da kashi 80 cikin dari, yawansu ta hanyar hasken rana ya ragu da kashi 90 cikin dari, wadanda suka aza tubalin yin amfani da irin wannan makamashi a fadin duniya. A halin yanzu, yawan na’urorin samar da makamashin da za a sabuntawa ya fi yawan na kwal, wannan wani babban canji ne a tsarin samar da makamashi. Sin za ta ci gaba da yin amfani da makamashin da za a iya sabuntawa don maye gurbin makamashin kwal da sauran burbushin halittu.

Wakilin Sin ya kara da cewa, Sin ta hada kai da kasashe da yankuna fiye da 100, kan ayyukan samar da makamashi masu tsabta, da daddale yarjejeniyoyin fahimtar juna kan hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa wajen tinkarar sauyin yanayi tare da kasashe masu tasowa fiye da 10. A nan gaba Sin za ta ci gaba da yin hadin gwiwa tare da kasashe masu tasowa don inganta hadin gwiwarsu a fannonin kudi da fasahohi. (Ibrahim Yaya, Zainab Zhang)

MDD
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Da Koriya Ta Arewa Na Fuskantar Sabbin Damammaki Da Kudurori In Ji Shugaba Xi Jinping
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Ta Yi Kira Ga EU Ta Hada Hannu Da Ita Domin Inganta Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakaninsu
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Ta Fara Wani Aikin Hanyar Ruwa A Kogi Mafi Tsawo Na 3 A Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Tattauna Da Kim Jong Un

MASU ALAKA

Sin Da Koriya Ta Arewa Na Fuskantar Sabbin Damammaki Da Kudurori In Ji Shugaba Xi Jinping
Daga Birnin Sin

Sin Da Koriya Ta Arewa Na Fuskantar Sabbin Damammaki Da Kudurori In Ji Shugaba Xi Jinping

June 8, 2026
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga EU Ta Hada Hannu Da Ita Domin Inganta Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakaninsu
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga EU Ta Hada Hannu Da Ita Domin Inganta Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakaninsu

June 8, 2026
Kasar Sin Ta Fara Wani Aikin Hanyar Ruwa A Kogi Mafi Tsawo Na 3 A Duniya
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Fara Wani Aikin Hanyar Ruwa A Kogi Mafi Tsawo Na 3 A Duniya

June 8, 2026
Next Post
Na Samu Farin Ciki Sosai A Farkon Fara Rubutuna – Fauziyya

Na Samu Farin Ciki Sosai A Farkon Fara Rubutuna - Fauziyya

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Ilimi Ne Babban Makamin Daƙile Ta’addanci — Ministan Tsaro

June 8, 2026
Sin Da Koriya Ta Arewa Na Fuskantar Sabbin Damammaki Da Kudurori In Ji Shugaba Xi Jinping

Sin Da Koriya Ta Arewa Na Fuskantar Sabbin Damammaki Da Kudurori In Ji Shugaba Xi Jinping

June 8, 2026
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga EU Ta Hada Hannu Da Ita Domin Inganta Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakaninsu

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga EU Ta Hada Hannu Da Ita Domin Inganta Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakaninsu

June 8, 2026
Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

Gwamnatin Borno Ta Musanta Biyan Kuɗin Fansa Domin Kuɓutar da Mutane 360

June 8, 2026
Kasar Sin Ta Fara Wani Aikin Hanyar Ruwa A Kogi Mafi Tsawo Na 3 A Duniya

Kasar Sin Ta Fara Wani Aikin Hanyar Ruwa A Kogi Mafi Tsawo Na 3 A Duniya

June 8, 2026
Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Dattawan Zamfara 50 Yayin Taron Sulhu A Cikin Daji

June 8, 2026
Xi Jinping Ya Tattauna Da Kim Jong Un

Xi Jinping Ya Tattauna Da Kim Jong Un

June 8, 2026
Yari Ya Dace Da Rayuwar Mulki Da Kasuwanci

Yari Ya Dace Da Rayuwar Mulki Da Kasuwanci

June 8, 2026
Me Kashim Imam Ke Yi A Yanzu?

Me Kashim Imam Ke Yi A Yanzu?

June 8, 2026
A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

June 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.