ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Ta Yi Rawar Gani Wajen Ingiza Ci Gaban Duniya Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

by CGTN Hausa
3 years ago
Sin

A yayin taron BRF da aka kammala, babban magatakardar MDD Antonio Guterres, ya yi jawabi da ya ja hankalin mahalarta taron, wanda a cikin sa ya bayyana manufar “Gina hanyar siliki ba tare da gurbata muhalli ba”, a matsayin matakin warware kalubalen da ake fuskanta, tare da share fagen tunkarar sabuwar turbar da za ta amfani bil adama, da ma duniyar da yake rayuwa cikin ta.

Cikin shekaru 10 da suka gabata, an gina tashar samar da lantarki ta hasken rana a tuddan kudancin Amurka, an kuma samar da tashar lantarki ta iska, mafi girma a yankin tsakiyar Asiya a hamadar Gobi, yayin da aka gina tashoshin samar da lantarki ta ruwa a kogin kudancin Asiya.

  • Sin Ta Yi Matukar Takaici Da Matakin Da Amurka Ta Dauka Na Dakatar Da Kudurin Jin Kai A Gaza
  • Zaben 2023: Takaddamar Kashi 94 Cikin 100 Na Kujerun Da Aka Lashe Ta Dora Shakku Kan INEC

Wadannan ayyukan hadin gwiwa da aka gudanar, karkashin shawarar ziri daya da hanya daya, sun saukaka wahalhalun da ake fuskanta ta fuskar karancin makamashi, kana matakin ya bunkasa amfani da makamashi mai tsafta, tare da samar da goyon baya ga manufar zamanantar da ci gaba a kasashen da ayyukan suka gudana.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, a shekarun 10, Sin ta gina shawarar ziri daya da hanya daya, karkashin tsarin hadakar kasashe, don samar da ayyukan ci gaba ba tare da lalata muhalli ba har sama da 150, tare da sama da kasashe 40, kana ta gina tsarin ziri daya da hanya daya, na hadin kai da abokan hulda a kasashe 32. Bugu da kari, ta yi alkawarin ba za ta gina sabbin tashoshin samar da lantarki masu amfani da kwal a kasashen ketare ba, wanda hakan ya zama babbar gudummawa da Sin din ke bayarwa, wajen bunkasa raya tattalin arzikin duniya bisa tsari mai dorewa, tare da rage fitar da iskar carbon mai dumama yanayi.

Yayin taron na BRF da ya kammala, Sin ta sanar da aniyar gudanar da wasu ayyuka 8, domin goyon baya ga gina ziri daya da hanya daya mai inganci, wanda daya daga cikin su shi ne bunkasa ci gaba maras gurbata yanayi. A kuma mataki na gaba, Sin za ta zage damtse wajen ingiza ci gaba maras gurbata muhalli, da samar da ci gaba ta hanyoyin rage fitar da iskar carbon, tare da sauran kasashe da suka shiga shawarar ziri daya da hanya daya, ta yadda za a kai ga cimma nasarar sauya fasalin masana’antu zuwa marasa gurbata yanayi. (Saminu Alhassan)

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

 

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Bai Kamata A Ce Shugaban Kasa Ne Yake Nada Shugaban INEC Ba – Jega

Bai Kamata A Ce Shugaban Kasa Ne Yake Nada Shugaban INEC Ba – Jega

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.