• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bai Kamata A Ce Shugaban Kasa Ne Yake Nada Shugaban INEC Ba – Jega

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Bai Kamata A Ce Shugaban Kasa Ne Yake Nada Shugaban INEC Ba – Jega
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), Farfesa Attahiru Jega, ya yi kira da a yi wa dokar zabe ta 2022 kwaskwarima.

Ya ce duk da cewa dokar zabe ta Nijeriya ita ce mafi inganci a tarihin kasar, amma ba ta cika ba; kuma akwai bukatar a kara yin gyare-gyare don kawar da shubuha da kuma karfafa wasu sassanta.

  • Sin Ta Yi Rawar Gani Wajen Ingiza Ci Gaban Duniya Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba
  • Wakilin Sin A MDD Ya Yi Kira Da A Aiwatar Da Matakan Gaggauta Dakatar Da Bude Wuta Tsakanin Falasdinu Da Isara’ila

Ya bayyana hakan ne a wani taron kwana biyu da cibiyar nazarin harkokin dimokaradiyya ta kasa (NILDS) ta shirya wa sanatoci a garin Ikot Ekpene, jihar Akwa Ibom.

Gyare-gyaren, in ji shi, ya kamata a gyara hanyar lantarki daga zabuka masu zuwa a shekarar 2027.

Ya kuma ce, bai kamata shugaban kasa ya sake samun ikon nada shugaban INEC da kwamishinonin hukumar na kasa ba domin kwato hukumar daga bangaranci.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kama Mutum 2 Da AK-47 A Taraba

Shugabannin Jam’iyyar ADC Na Jihohi 36 Da Abuja Sun Bayyana Goyon Bayansu Ga David Mark

Ya ce kamata ya yi a sake duba dokar domin tabbatar da cewa an warware duk wasu batutuwan da suka taso a kan gudanar da zabe tare da yanke hukunci kafin ranar da za a rantsar da su.

Masu ruwa da tsaki da dama sun bayyana damuwarsu kan yadda sashe na 64 na dokar zabe, wanda ya bayyana yadda ake yada sakamakon zaben, na da saukin magudi.

Sai dai Jega ya ce ya kamata a fayyace sashen ta hanyar wajabta watsa sakamakon zabe, gami da dora sakamakon matakin zabe da takardar sakamakon da ake amfani da shi a matakai daban-daban na tattara sakamakon zabe.

“INEC za ta samu isasshen lokacin da za ta shirya aiwatar da wannan, idan an yi wa dokar kwaskwarima da wuri a zaben da ke tafe,” in ji shi.

Ya kuma yi kira da a bullo da yanayin fara kada kuri’a ga wadanda suka cancanci kada kuri’a, kamar ma’aikatan INEC, masu sa ido da direbobinsu, jami’an tsaro, da ‘yan jarida ko kuma wani tsari na musamman da zai ba su damar kada kuri’a a ranar zabe, musamman zaben shugaban kasa.

Tsohon shugaban na INEC ya bayar da shawarar cewa ‘yan kasashen waje su kada kuri’a, musammam zaben shugaban kasa, don bai wa ‘yan kasa damar kada kuri’a, musamman wadanda ke aiki a kasashen waje.

Ya ce, “Akwai bukatar a sanya tsauraran sharudan janyewar dan takara da kuma maye gurbinsa don hana cin zarafi. Ba wa INEC damar tantancewa da kuma idan ya cancanta ta haramta wa ‘yan takarar da shaidarsu ta nuna cewa ba su cancanta ba.

“Akwai bukatar doka ta ba wa ‘yan takara da ke wajen jam’iyyun siyasa dama, da kuma ‘yan kasa masu biyan haraji su shigar da kara a kan ‘yan takarar da ke bai wa INEC bayanan karya game da takararsu.

“Duk da cewa sashe na 132(8) & (9) ya bayar da wa’adin da kotuna da kotunan daukaka kara za su yanke hukunci, akwai bukatar musamman dangane da zababbun mukaman zartarwa, a tabbatar da an warware dukkan shari’o’i da kuma yanke hukunci a gabanin. ranar rantsuwa.

“Bincika tsarin nade-naden mukamai a INEC, musamman don karfin shugaban kasa wajen nada shugaban INEC da kwamishinonin INEC na kasa, domin kubutar da hukumar daga mummunan zato da ake maga.

“Ya kamata a samar da ka’idoji don gabatar da koke-koke ga duk wanda aka zaba yayin wannan aikin.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HukunciINECJegaShari'aZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Yi Rawar Gani Wajen Ingiza Ci Gaban Duniya Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Next Post

“Hanyar Siliki Ta Dijital” Na Ingiza Zamanantar Da Duniya

Related

Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mutum 2 Da AK-47 A Taraba

15 hours ago
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista
Manyan Labarai

Shugabannin Jam’iyyar ADC Na Jihohi 36 Da Abuja Sun Bayyana Goyon Bayansu Ga David Mark

18 hours ago
Matatun Man Fetur Na Nijeriya Ba Za Su Ci Gaba Da Aiki Yadda Ya Kamata Ba – Dangote
Manyan Labarai

Matatun Man Fetur Na Nijeriya Ba Za Su Ci Gaba Da Aiki Yadda Ya Kamata Ba – Dangote

19 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Wa ‘Yansanda Hari Tare Da Kashe Wani Mutum Da Raunata Wani A Nasarawa

20 hours ago
An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa
Manyan Labarai

An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

20 hours ago
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa
Manyan Labarai

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

1 day ago
Next Post
“Hanyar Siliki Ta Dijital” Na Ingiza Zamanantar Da Duniya

“Hanyar Siliki Ta Dijital” Na Ingiza Zamanantar Da Duniya

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

July 12, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.