ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bai Kamata A Ce Shugaban Kasa Ne Yake Nada Shugaban INEC Ba – Jega

by Sadiq
3 years ago
INEC

Tsohon Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), Farfesa Attahiru Jega, ya yi kira da a yi wa dokar zabe ta 2022 kwaskwarima.

Ya ce duk da cewa dokar zabe ta Nijeriya ita ce mafi inganci a tarihin kasar, amma ba ta cika ba; kuma akwai bukatar a kara yin gyare-gyare don kawar da shubuha da kuma karfafa wasu sassanta.

  • Sin Ta Yi Rawar Gani Wajen Ingiza Ci Gaban Duniya Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba
  • Wakilin Sin A MDD Ya Yi Kira Da A Aiwatar Da Matakan Gaggauta Dakatar Da Bude Wuta Tsakanin Falasdinu Da Isara’ila

Ya bayyana hakan ne a wani taron kwana biyu da cibiyar nazarin harkokin dimokaradiyya ta kasa (NILDS) ta shirya wa sanatoci a garin Ikot Ekpene, jihar Akwa Ibom.

ADVERTISEMENT

Gyare-gyaren, in ji shi, ya kamata a gyara hanyar lantarki daga zabuka masu zuwa a shekarar 2027.

Ya kuma ce, bai kamata shugaban kasa ya sake samun ikon nada shugaban INEC da kwamishinonin hukumar na kasa ba domin kwato hukumar daga bangaranci.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Ya ce kamata ya yi a sake duba dokar domin tabbatar da cewa an warware duk wasu batutuwan da suka taso a kan gudanar da zabe tare da yanke hukunci kafin ranar da za a rantsar da su.

Masu ruwa da tsaki da dama sun bayyana damuwarsu kan yadda sashe na 64 na dokar zabe, wanda ya bayyana yadda ake yada sakamakon zaben, na da saukin magudi.

Sai dai Jega ya ce ya kamata a fayyace sashen ta hanyar wajabta watsa sakamakon zabe, gami da dora sakamakon matakin zabe da takardar sakamakon da ake amfani da shi a matakai daban-daban na tattara sakamakon zabe.

“INEC za ta samu isasshen lokacin da za ta shirya aiwatar da wannan, idan an yi wa dokar kwaskwarima da wuri a zaben da ke tafe,” in ji shi.

Ya kuma yi kira da a bullo da yanayin fara kada kuri’a ga wadanda suka cancanci kada kuri’a, kamar ma’aikatan INEC, masu sa ido da direbobinsu, jami’an tsaro, da ‘yan jarida ko kuma wani tsari na musamman da zai ba su damar kada kuri’a a ranar zabe, musamman zaben shugaban kasa.

Tsohon shugaban na INEC ya bayar da shawarar cewa ‘yan kasashen waje su kada kuri’a, musammam zaben shugaban kasa, don bai wa ‘yan kasa damar kada kuri’a, musamman wadanda ke aiki a kasashen waje.

Ya ce, “Akwai bukatar a sanya tsauraran sharudan janyewar dan takara da kuma maye gurbinsa don hana cin zarafi. Ba wa INEC damar tantancewa da kuma idan ya cancanta ta haramta wa ‘yan takarar da shaidarsu ta nuna cewa ba su cancanta ba.

“Akwai bukatar doka ta ba wa ‘yan takara da ke wajen jam’iyyun siyasa dama, da kuma ‘yan kasa masu biyan haraji su shigar da kara a kan ‘yan takarar da ke bai wa INEC bayanan karya game da takararsu.

“Duk da cewa sashe na 132(8) & (9) ya bayar da wa’adin da kotuna da kotunan daukaka kara za su yanke hukunci, akwai bukatar musamman dangane da zababbun mukaman zartarwa, a tabbatar da an warware dukkan shari’o’i da kuma yanke hukunci a gabanin. ranar rantsuwa.

“Bincika tsarin nade-naden mukamai a INEC, musamman don karfin shugaban kasa wajen nada shugaban INEC da kwamishinonin INEC na kasa, domin kubutar da hukumar daga mummunan zato da ake maga.

“Ya kamata a samar da ka’idoji don gabatar da koke-koke ga duk wanda aka zaba yayin wannan aikin.”

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
“Hanyar Siliki Ta Dijital” Na Ingiza Zamanantar Da Duniya

“Hanyar Siliki Ta Dijital” Na Ingiza Zamanantar Da Duniya

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.