• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin: Ya Kamata Burtaniya Ta Mutunta Gaskiya Kuma Ta Daina Nuna Rashin Adalci

by CMG Hausa
3 years ago
Sin

Dangane da zargin da firaministan kasar Burtaniya Rishi Sunak ya yi kan manufar kasar Sin, game da riga kafin yaduwar annobar COVID-19, ciki har da duka da kame wani wakilin BBC, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Zhao Lijian, ya bayyana a yau Talata 29 ga wata cewa, irin kalaman na Burtaniya sun sabawa gaskiyar lamarin, tare da tsoma baki cikin harkokin gidan kasar Sin, kuma Sin tana adawa da hakan.

Kakakin ya bayyana cewa, ainihin lamarin shi ne, a daren ranar 27 ga wata, domin kiyaye zaman lafiyar al’umma, ‘yan sandan birnin Shanghai sun lallashi mutanen da suka taru a wata mararrabar hanya, da su bar wurin kamar yadda doka ta tanada, ciki har da ‘dan jaridar BBC dake Shanghai.

  • Shugaban Kasar Sin Ya Sha Alwashin Karfafa Hadin Gwiwar Kasarsa Da Rasha A Fannin Makamashi

Ko da yake ‘yan sandan sun bayyana wa ‘dan jaridar karara cewa, suna shirin lallashin mutanen da ke wurin domin su tafi, amma ‘dan jaridar ya ki barin wurin, kuma bai bayyana wa ‘yan sanda matsayinsa na ‘dan jaridar ba.

Don haka, ‘yan sandan suka tafi da shi ala tilas, kana daga bisani suka umurce shi da ya tafi bayan gudanar da tantancewar da ta dace da sanar da shi doka, kuma an aiwatar da hakan ne bisa tsarin dokoki da ka’idoji.

Kakakin ya jaddada cewa, ‘yan jarida na kasashen waje suna da hakkin ruwaito rahotanni bisa doka a kasar Sin, kuma dole ne su bi dokokin kasar Sin, kana ya kamata su nuna katin aikin jarida kafin su bayar da rahoto, kuma bai kamata su aiwatar da wasu ayyukan da ba su dace da matsayinsu ba, kuma hakan ya shafi duk wata kafa ta watsa labarai, kana hakan bai saba da abin da ake kira da ‘yancin aikin jarida ba.

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kakakin ya kara bayyana cewa, akwai kafafen yada labarai na kasashen waje da yawa a kasar Sin, abun tambaya shi ne me ya sa har kullum BBC ke samun matsala? Wannan batu ne da ya kamata a yi la’akari da shi sosai. (Mai fassara: Bilkisu Xin)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi
Daga Birnin Sin

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Next Post
An Harba kuKmbon Shenzhou-15 Dauke Da ‘Yan Sama Jannati 3

An Harba kuKmbon Shenzhou-15 Dauke Da ‘Yan Sama Jannati 3

LABARAI MASU NASABA

Triumph

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.