• Leadership Hausa
Saturday, April 1, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin: Ya Kamata Burtaniya Ta Mutunta Gaskiya Kuma Ta Daina Nuna Rashin Adalci

by CMG Hausa
4 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin: Ya Kamata Burtaniya Ta Mutunta Gaskiya Kuma Ta Daina Nuna Rashin Adalci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dangane da zargin da firaministan kasar Burtaniya Rishi Sunak ya yi kan manufar kasar Sin, game da riga kafin yaduwar annobar COVID-19, ciki har da duka da kame wani wakilin BBC, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Zhao Lijian, ya bayyana a yau Talata 29 ga wata cewa, irin kalaman na Burtaniya sun sabawa gaskiyar lamarin, tare da tsoma baki cikin harkokin gidan kasar Sin, kuma Sin tana adawa da hakan.

Kakakin ya bayyana cewa, ainihin lamarin shi ne, a daren ranar 27 ga wata, domin kiyaye zaman lafiyar al’umma, ‘yan sandan birnin Shanghai sun lallashi mutanen da suka taru a wata mararrabar hanya, da su bar wurin kamar yadda doka ta tanada, ciki har da ‘dan jaridar BBC dake Shanghai.

  • Shugaban Kasar Sin Ya Sha Alwashin Karfafa Hadin Gwiwar Kasarsa Da Rasha A Fannin Makamashi

Ko da yake ‘yan sandan sun bayyana wa ‘dan jaridar karara cewa, suna shirin lallashin mutanen da ke wurin domin su tafi, amma ‘dan jaridar ya ki barin wurin, kuma bai bayyana wa ‘yan sanda matsayinsa na ‘dan jaridar ba.

Don haka, ‘yan sandan suka tafi da shi ala tilas, kana daga bisani suka umurce shi da ya tafi bayan gudanar da tantancewar da ta dace da sanar da shi doka, kuma an aiwatar da hakan ne bisa tsarin dokoki da ka’idoji.

Kakakin ya jaddada cewa, ‘yan jarida na kasashen waje suna da hakkin ruwaito rahotanni bisa doka a kasar Sin, kuma dole ne su bi dokokin kasar Sin, kana ya kamata su nuna katin aikin jarida kafin su bayar da rahoto, kuma bai kamata su aiwatar da wasu ayyukan da ba su dace da matsayinsu ba, kuma hakan ya shafi duk wata kafa ta watsa labarai, kana hakan bai saba da abin da ake kira da ‘yancin aikin jarida ba.

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Irin Su Na Farko A Duniya

Kasar Sin Ta Bayar Da Shawarwari Dangane Da Yadda Za A Aiwatar Da Sanarwar Vienna Yadda Ya Kamata

Kakakin ya kara bayyana cewa, akwai kafafen yada labarai na kasashen waje da yawa a kasar Sin, abun tambaya shi ne me ya sa har kullum BBC ke samun matsala? Wannan batu ne da ya kamata a yi la’akari da shi sosai. (Mai fassara: Bilkisu Xin)

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Harbe Shugabar Matan Jam’iyyar LP A Jihar Kaduna

Next Post

An Harba kuKmbon Shenzhou-15 Dauke Da ‘Yan Sama Jannati 3

Related

Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Irin Su Na Farko A Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Irin Su Na Farko A Duniya

8 hours ago
Kasar Sin Ta Bayar Da Shawarwari Dangane Da Yadda Za A Aiwatar Da Sanarwar Vienna Yadda Ya Kamata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bayar Da Shawarwari Dangane Da Yadda Za A Aiwatar Da Sanarwar Vienna Yadda Ya Kamata

9 hours ago
Ana Fatan A Hada Kai Wajen Shawo Kan Kalubalen Dake Addabar Duniya
Daga Birnin Sin

Ana Fatan A Hada Kai Wajen Shawo Kan Kalubalen Dake Addabar Duniya

10 hours ago
Taron Kolin Demokuradiyya Na Amurka Ya Shaidawa Duniya Ma’auni Biyu Da Amurka Ta Dauka Kan Batun Demokuradiyya
Daga Birnin Sin

Taron Kolin Demokuradiyya Na Amurka Ya Shaidawa Duniya Ma’auni Biyu Da Amurka Ta Dauka Kan Batun Demokuradiyya

11 hours ago
Boao: Kasar Sin Ta Karfafa Gwiwar Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Boao: Kasar Sin Ta Karfafa Gwiwar Kasa Da Kasa

12 hours ago
Shugaban Kasar Sin Ya Gana Da Firaministan Spaniya Da Na Malaysia Da Na Singapore
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Ya Gana Da Firaministan Spaniya Da Na Malaysia Da Na Singapore

12 hours ago
Next Post
An Harba kuKmbon Shenzhou-15 Dauke Da ‘Yan Sama Jannati 3

An Harba kuKmbon Shenzhou-15 Dauke Da ‘Yan Sama Jannati 3

LABARAI MASU NASABA

An Yanke Wa Wasu ‘Yan China 2 Hukuncin Daurin Shekaru 12 A Sakkwato

An Yanke Wa Wasu ‘Yan China 2 Hukuncin Daurin Shekaru 12 A Sakkwato

March 31, 2023
Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Irin Su Na Farko A Duniya

Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Irin Su Na Farko A Duniya

March 31, 2023
Zababben Gwamnan Katsina Ya Gana Da Buhari, Ya Ce Matsalar Tsaro Zai Fi Bai Wa Muhimmanci 

Zababben Gwamnan Katsina Ya Gana Da Buhari, Ya Ce Matsalar Tsaro Zai Fi Bai Wa Muhimmanci 

March 31, 2023
Kasar Sin Ta Bayar Da Shawarwari Dangane Da Yadda Za A Aiwatar Da Sanarwar Vienna Yadda Ya Kamata

Kasar Sin Ta Bayar Da Shawarwari Dangane Da Yadda Za A Aiwatar Da Sanarwar Vienna Yadda Ya Kamata

March 31, 2023
Mutum 14 Sun Shiga Hannun ‘Yan Sanda A Kano Kan Aikata Fashi Da Makami

Mutum 14 Sun Shiga Hannun ‘Yan Sanda A Kano Kan Aikata Fashi Da Makami

March 31, 2023
Ana Fatan A Hada Kai Wajen Shawo Kan Kalubalen Dake Addabar Duniya

Ana Fatan A Hada Kai Wajen Shawo Kan Kalubalen Dake Addabar Duniya

March 31, 2023
Ba Zan Tsoma Baki A Gwamnatin Abba Ba –Kwankwaso

Ba Zan Tsoma Baki A Gwamnatin Abba Ba –Kwankwaso

March 31, 2023
Taron Kolin Demokuradiyya Na Amurka Ya Shaidawa Duniya Ma’auni Biyu Da Amurka Ta Dauka Kan Batun Demokuradiyya

Taron Kolin Demokuradiyya Na Amurka Ya Shaidawa Duniya Ma’auni Biyu Da Amurka Ta Dauka Kan Batun Demokuradiyya

March 31, 2023
Har Yanzu Ni Ke Da Cikakken Iko A Matsayin Gwamnan Kano —Ganduje Ga Abba Gida-Gida

Har Yanzu Ni Ke Da Cikakken Iko A Matsayin Gwamnan Kano —Ganduje Ga Abba Gida-Gida

March 31, 2023
Boao: Kasar Sin Ta Karfafa Gwiwar Kasa Da Kasa

Boao: Kasar Sin Ta Karfafa Gwiwar Kasa Da Kasa

March 31, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.