• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin: Ya Kamata Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Da Afirka Ta Kasance Cikin Adalci, Daidaito Kuma A Bayyane

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Sin

An kammala taron kolin dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka na Beijing. A yayin taron manema labarai na yau, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning, ta yi martani kan yadda wasu kafofin yada labaru na kasashen yammacin duniya ke zuzuta batun bashin da ake bin kasashen Afirka, inda ta ce, tun bayan da aka kafa dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka shekaru 24 da suka gabata, dandalin ya taka muhimmiyar rawa wajen sa kaimi ga bunkasuwar kasashen Afirka, da inganta rayuwar jama’ar Afirka, wanda ke taimakawa Afirka warware sarkakiyar dake tattare da samun ci gaba da matsalar bashi. A yayin taron, shugabannin Afirka da dama ciki har shugaban kasar Afirka ta Kudu Cyril Ramophosa, sun bayyana cewa, jarin da kasar Sin ke zubawa a Afirka, bisa hadin gwiwa ce ta moriyar juna, kuma ba zai jefa Afirka cikin “tarkon bashi” ba.

 

Mao Ning ta jaddada cewa, kasar Sin ba ta taba zama babbar mai baiwa Afirka rancen kudi ba. Bisa kididdigar da bankin duniya ya fitar, a cikin basussukan da ake bin kasashen Afirka, yawan basussukan da kasashen Afirka suka karba daga bangarori da dama da masu ba da lamuni da bashi masu zaman kansu ya kai kashi 80 cikin 100, yayin da basussukan da ke tsakanin bangarorin biyu ke daukar kaso mara yawa. Duk da haka, a ko da yaushe kasar Sin tana taimakawa Afirka wajen sassauta matsin lamba da yafe basussuka a tsakanin bangarori biyu da ma tsakanin bangarori daban-daban, kuma ita ce kasar da ta fi ba da gudummawa ga shirin yafe basussuka na G20. A cikin shirin aikin da aka amince da shi a wannan taro, kasar Sin ta kuma gabatar da shawarar wasu matakai na yafe basussuka.

 

Mao Ning ta kara da cewa muna kira ga kasashen duniya, musamman kasashen da suka ci gaba, da cibiyoyin hada-hadar kudi na kasa da kasa, da su sauke nauyin da ya rataya a wuyansu, da taimakawa kasashen Afirka wajen sauke nauyin basussuka, da samun ci gaba mai dorewa. (Yahaya)

LABARAI MASU NASABA

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya
Daga Birnin Sin

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103
Daga Birnin Sin

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Next Post
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Shaida Cewa Ba Lallai Ba Ne A Ci Nasara Daga Faduwar Wani Bangare Ba

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Shaida Cewa Ba Lallai Ba Ne A Ci Nasara Daga Faduwar Wani Bangare Ba

LABARAI MASU NASABA

An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

October 19, 2025
Nijar

Gwamnatin Nijar Ta Yaye Tsofaffin Mayaka 369 Da Aka Bai Wa Horon Sauya Tunani

October 19, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

‘Yan Siyasa 11 Da Suka Faɗa Dambarwar Takardar Shaidar Karatu Ta Bogi

October 19, 2025
gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
ASUU

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.