ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, November 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sir Sherard Cowper-Coles: Biritaniya Da Sin Suna Amfana Daga Karuwar Dangantakar Tattalin Arziki Da Cinikayya

by CMG Hausa
2 years ago
Sir Sherard Cowper-Coles

Yayin wata hira ta musamman ta kafar bidiyo da ya yi da manema labarai, na kamfanin dillancin labarai na Xinhua na kasar Sin a baya-bayan nan, Sir Sherard Cowper-Coles, shugaban majalisar harkokin kasuwanci tsakanin Sin da Birtaniya, ya ce kasashen Birtaniya da Sin, za su ci gajiyar kud-da-kut a fannin zuba jari da huldar kasuwanci. Ya yi amfani da wani karin magana na Turancin Ingilishi, dake bayyana cewa, “Karuwar ruwa a teku na taimakawa tafiyar jirgin ruwa.” 

Sherard Cowper-Coles ya ce “manyan jiragen ruwa biyu na Biritaniya da Sin, za su yi shawagi da kyau a ruwa mai karuwar wadata”.

  • Cinikayyar Albarkatun Gona Na Kasar Sin Da Kasashen Ketare Ta Karu Da Kaso 6.4 Bisa Dari A Rabin Shekarar Bana 

A kwanan baya, Sherard Cowper-Coles, da sauran wakilan majalisar harkokin kasuwanci na Sin da Birtaniya sun ziyarci wasu biranen kasar Sin, ciki har da Shenzhen, da Shanghai, da Beijing da kuma Guangzhou. Bayan rangadin na su, Cowper-Coles ya bayyana cewa, ya gano cewa, kamfanonin Birtaniya dake kasar Sin, sun fi kyautata zaton samun bunkasuwar kasuwannin kasar Sin.

ADVERTISEMENT

Ya ce, a shekarar 2022, yawan cinikayyar da ke tsakanin kasashen Birtaniya da Sin ya kai wani sabon matsayi, kuma dangantakar tattalin arziki da cinikayya tsakanin kasashen biyu ta shiga wani sabon mataki. Cowper-Coles ya kara da cewa, sana’o’i da yawa na Birtaniya suna da damar samun ci gaba sosai a kasuwannin kasar Sin, kaza lika kayayyakin da suka hada da motoci, da tufafi, da kifin salmon, na samun karbuwa sosai ga masu sayayya na kasar Sin. A sa’i daya kuma, kasar Birtaniya ita ma na shigo da tarin kayayyaki daga kasar ta Sin.

Da yake magana kan fannonin zuba jari da ake da damar yin hadin gwiwa a tsakanin kasashen biyu, Cowper-Coles ya ce, kasashen Birtaniya da Sin sun dukufa, wajen cimma burin rage gurbata muhalli. Bugu da kari, karuwar bukatun kiwon lafiya na masayan kayan kasar Sin, na samar da damammaki ga kamfanonin Burtaniya a fannonin kiwon lafiya, da kimiyyar rayuwa da dai sauransu. Ya kuma yi maraba da yadda kasar Sin ke ci gaba da inganta bude kofa a fannin harkokin kudi. (Mai fassara: Bilkisu Xin)

LABARAI MASU NASABA

An Kaddamar Da Babbar Hanyar Mota Da Sin Ta Tallafa Wajen Ginawa A Namibia

An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Kaddamar Da Babbar Hanyar Mota Da Sin Ta Tallafa Wajen Ginawa A Namibia
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Babbar Hanyar Mota Da Sin Ta Tallafa Wajen Ginawa A Namibia

November 11, 2025
An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 
Daga Birnin Sin

An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

November 10, 2025
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

November 10, 2025
Next Post
Kiris Mahaifina Ya Sa A Kama Wanda Ya Fara Sa Ni Fim Amma… – Maryam Kimono

Kiris Mahaifina Ya Sa A Kama Wanda Ya Fara Sa Ni Fim Amma… - Maryam Kimono

LABARAI MASU NASABA

APC

Sauya Sheƙa: Yadda APC Ke Ci Gaba Da Hamɓarar Da Jam’iyyun Adawa A Majalisa

November 11, 2025
An Kaddamar Da Babbar Hanyar Mota Da Sin Ta Tallafa Wajen Ginawa A Namibia

An Kaddamar Da Babbar Hanyar Mota Da Sin Ta Tallafa Wajen Ginawa A Namibia

November 11, 2025
‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP

Kotu Ta Sake Hana PDP Gudanar Da Babban Taronta Na Ƙasa

November 11, 2025
‘Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Kashe Ɗan Wasan Barau FC A Katsina

‘Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Kashe Ɗan Wasan Barau FC A Katsina

November 11, 2025
Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

November 11, 2025
HOTUNA: Yadda Gobara Ta Ƙone Shaguna 25 A Kasuwar Singa A Kano

HOTUNA: Yadda Gobara Ta Ƙone Shaguna 25 A Kasuwar Singa A Kano

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

November 11, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Faɗa Ya Kaure Tsakanin Boko Haram Da ISWAP, An Kashe Mayaƙa Sama Da 170

November 11, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Yi Barazanar Maka BBC A Kotu Tare Da Neman Diyyar $1bn

November 11, 2025
Rashin Aiki Ga Matasa Babbar Barazana Ce Ga Nijeriya – Obasanjo 

Obasanjo Ya Buƙaci Matasa Su Karɓi Ragamar Shugabanci A Ƙasashen Afrika

November 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.