• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Siyasar Ubangida: Baya Ta Haihu A Jihar Ribas

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Labarai
0
Siyasar Ubangida: Baya Ta Haihu A Jihar Ribas
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An samu takaddamar siyasa a garin Fatakwal, Babban Birnin Jihar Ribas, sakamakonn yunkurin tsige gwamnan jihar, Siminalayi Fubara, da wasu ‘yan masalisar dokokin jihar suka yi, wadanda ake zargin masu biyya ne ga ministan Abuja, Nyesom Wike.

Lamarin ya yi tsami har sai da Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya shiga tsakanin rikicin siyasar Jihar Ribas da ta kunno kai.

  • Baje Kolin CIIE Na Kara Jan Hankalin Sassa Kasa Da Kasa
  • Zamu Sabanta Dakin Karatu Na Sashen Harsunan Nijeriya Na Jami’ar Bayero — Hassan Baita

Dangantaka dai ta yi tsami tsakanin Gwamna Fubara da wanda ya gada, Wike wanda a halin yanzu yake rike da mukamin ministan Babban Birnin Tarayya Abuja.

Siyasan ubangida yana matukar take muhimmiyar rawa a cikin siyasar Nijeriya, wanda wannan ba sabon al’amari ba ne a domin an samu irin wannan lamari a mafi yawancin jihohin kasar nan.

‘Yan siyasan Nijeriya sukan kokarin kafa yaransu a lokacin da wa’adin mulkinsu ya kusan shudewa tare da tsammanin yi musu biyya a gare su.

Labarai Masu Nasaba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

Duk da hakan, wannan kokari kan dore a wasu lokuta, yayin da a wasu lokutan kuma ake yin baran-baran a tsakanin ubangida da yaronsa na siyasa.

Da wasu daga cikin ‘yan siyasan Nijeriya da suka raba gari a tsakanin ubangida da yaronsa na siyasa.

Nyesom Wike Da Rotimi Amaechi

Nyesom Wike da Rotimi Amaechi sun taba zama abokan juna. Inda Amaechi ya goyi bayan Wike na zama gwamnan Jihar Ribas. Sai dai alakar tasu ta wargaje a lokacin zaben 2015. Amaechi da gwamna mai ci sun mara wa Dakuku Peterside baya, a matsayin wanda zai gaje shi, yayin da Wike, tsohon shugaban ma’aikatan Amaechi, suka tsaya takara a karkashin tutar jam’iyyar PDP, kuma suka yi nasara. Wannan bambancin dai ya janyo zargin juna, inda Wike ya yi zargin cin hanci da rashawa a kan Amaechi da kuma sukar sa kan rashin kula da jin dadin jihar.

Godwin Obaseki Da Adams Oshiomhole

Godwin Obaseki da Adams Oshiomhole sun taba zama ubangida da yaro a Jihar Edo. Oshiomhole, tsohon gwamnan ya goyi bayan takarar Obaseki a matsayin wanda zai gaje shi. Sai dai kuma bayan da Obaseki ya hau kan karagar mulki, rikici ya kaure a tsakaninsu. Oshiomhole ya zargi Obaseki da rashin mutuntawa tare da yin watsi da mai gidansa, wanda hakan janyo yunkurin tsige Obaseki daga kujerar gwamnan Jihar Edo a 2020.

Abdullahi Ganduje Da Rabiu Kwankwaso

Abdullahi Ganduje da Rabiu Kwankwaso sun yi kawancen siyasa a Jihar Kano. Kwankwaso, tsohon gwamnan ya amince da Ganduje a matsayin wanda zai gaje shi. Sai dai alakarsu ta yi tsami ne bayan rantsar da Ganduje a matsayin gwamnan Jihar Kano. Kwankwaso ya zargin Ganduje da cin hanci da rashawa, ya kuma soki Ganduje da kin bin shawararsa, wanda hakan ya sa Kwankwaso ya sauya sheka daga jam’iyyar APC zuwa jam’iyyar PDP, daga baya kuma sa koma jam’iyyar NNPP.

Peter Obi Da Chris Ngige

Peter Obi da Chris Ngige sun taba zaman ubangida da yaro a siyasar a Jihar Anambra. Ngige ya kasance tsohon gwamnan, yayin da ya goyi bayan Obi a matsayin magajinsa. Sai dai kuma dangantar tasu ta tabarbare bayan Obi ya hau kan karagar mulki. Ngige ya zargi Obi da cin hanci da rashawa da rashin bin ubangidansa, wanda hakan ya sa Ngige ya fice daga PDP zuwa APC.

Bukola Saraki Da Shugabanin PDP Na Kwara

Bukola Saraki da jiga-jigan PDP na Jihar Kwara sun kasance abokan siyasa na kut da kut a baya. Shugabannin jam’iyyar PDP na Jihar Kwara, karkashin jagorancin tsohon gwamnan jihar, Sanata Shaaba Lafiagi, sun goyi bayan Saraki ya zama gwamna. Sai dai alakar bangarorin biyu ta yi tsami bayan rantsar da Saraki. Saraki ya zargi shugabannin jam’iyyar PDP na Jihar Kwara da cin hanci da rashawa da kuma kokarin shawo kansa ta hanyar da ba ta dace ba. Rikicin da barke tsakanin bangarorin biyu wanda ya kai ga ficewar Saraki daga PDP zuwa APC. Sai dai daga baya Saraki ya koma PDP.

Aminu Tambuwal Da Aliyu Wamakko

Aminu Tambuwal da Aliyu Wamakko sun taba zama ubangida da yaro a fagen siyasar Jihar Sakkwato. Wamakko wanda ya kasance tsohon gwamnan ya goyi bayan Tambuwal a matsayin wanda zai gaje shi. Sai dai dangantakarsu ta yi tsami bayan rantsar da Tambuwal a matsayin gwamna. Wamakko ya zargi Tambuwal da rashin mutunta ubangidansa. Wannan rashin jituwa ta sa Tambuwal ya sauya sheka daga jam’iyyar PDP zuwa APC, inda daga baya koma.

Olusegun Mimiko Da Adebayo Adefarati

Olusegun Mimiko da Marigayi Adebayo Adefarati a baya sun kasance ubangida da yaron siyasa. Adefarati, tsohon gwamnan Jihar Ondo, ya goyi bayan Mimiko na neman kujerar gwamna. Duk da haka, dangantakarsu ta yi tsami bayan Mimiko ta hau kan karagar mulki na gwamnan Jihar Ondo. Adefarati ya yi zargin rashin mutuntawa da kuma yin watsi da shawararsa, wanda hakan ya haifar da sabani a tsakaninsu. Wannan rashin jituwa ya sa Adefarati ya sauya sheka daga jam’iyyar adawa ta AD zuwa jam’iyyar PDP.

Daga cikin wadannan za ku iya fahimtar cewa rikicin siyasar da ke faruwa a yanzu tsakanin Nyesom Wike da Sim Fubara ba sabon abu bane a fagen siyasar Nijeriya. Haka nan ana iya lura da yanayin sauya sheka a tsakanin ‘yan siyasan Nijeriya sakamakon rashin jutuwa, sannan kuma za a iya hasashen yiwuwar maimaita irin wannan lamari a cikin ‘yan siyasar PDP na Jihar Ribas.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

A Sake Tunani Game Da Karin Kudin Makaranta A Nijeriya

Next Post

Rabon Tallafin Rage Radadi: Wane Hali Ake Ciki?

Related

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

2 hours ago
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye
Labarai

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

4 hours ago
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
Manyan Labarai

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

5 hours ago
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

6 hours ago
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja
Labarai

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

8 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

9 hours ago
Next Post
Rabon Tallafin Rage Radadi: Wane Hali Ake Ciki?

Rabon Tallafin Rage Radadi: Wane Hali Ake Ciki?

LABARAI MASU NASABA

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

September 18, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

September 18, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.