Dakarun Soji sun kashe wani babban kwamandan Boko Haram mai suna Malam Jidda a wani haɗin gwiwar farmaki da suka kai ta ƙasa da sama a Jihar Yobe.
Rundunar Operation Haɗin Kai tare da taimakon rundunar sojin sama ne suka kaddamar da wannan farmaki a Ngazalgana, cikin Karamar Hukumar Gujba, ranar 9 ga Yuni, 2025.
- Mataimakin Firaministan Sin Ya Gana Da Ministar Kudin Birtaniya
- Shin Rashin Nasara Ya Rage Damar Yamal Na Ballon d’Or?
A cewar sanarwar da mai magana da yawun rundunar Operation Hadin Kai, Reuben Kovangiya ya fitar, Malam Jidda shi ne shugaban ƙauyukan Ngorgore da Malumti.
An kashe shi tare da wasu mayaƙan Boko Haram lokacin da dakarun suka kai hari.
Wasu daga cikin ‘yan ta’addan sun tsere da raunin harbin bindiga.
A wani samame da aka kai a Mallamfatori, cikin Karamar Hukumar Abadam, sojojin sun gano ƙarin gawarwakin ‘yan ta’adda da kuma tarin makamai.
Kayayyakin da aka ƙwato sun haɗa da bindigogi ƙirar AK-47, babura, harsasai masu yawa, ma’ajin harsasai, bututun roka, bom na hannu, rediyon hannu da wasu kayayyakin soji.
Rundunar sojin ta ce waɗannan hare-hare na baya-bayan nan na nuna ƙwazon da ake yi wajen murƙushe Boko Haram da ISWAP tare da dawo da zaman lafiya a yankin Arewa Maso Gabas.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp