Sojojin Nijeriya sun kashe wani shugaban ‘yan ta’adda Mai Dada a yankin Maru na jihar Zamfara yayin wani farmaki na musamman.
Babban hafsan Soja Manjo Janar Markus Kangye ya bayyana cewa an kama wasu waɗanda ake zargin suna kai wa ‘yan ta’adda kayayyaki, tare da aika wasu masu basu bayanai a jihohin Borno, Kaduna da Edo.
- Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17
- Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga
A Borno, Sojoji sun kashe ‘yan ta’adda uku tare da ƙwato makamai da harsasai da dama, yayin da aka kama wanda ake zargin jigilar kayayyakin ga ‘yan ta’adda a Monguno.
An kuma ƙwato bindigogi da harsasai a jihohin Kaduna da Filato, yayin da aka kama wasu ƴan fashi a Edo da Bayelsa.