• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Son Zuciyar Wasu Tsiraru Ya Haddasa Rashin Tsaro A NIjeriya – Alhaji Ibrahim

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Labarai
0
Son Zuciyar Wasu Tsiraru Ya Haddasa Rashin Tsaro A NIjeriya – Alhaji Ibrahim
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ganin yadda matsalar tsaro ta ki ci ta ki cinyewa, Shugaban gamayyar kungiyoyin matasan arewa mazauna Legas, Alhaji Ibrahim Ya’u Galadanci ya bayyana cewa son zuciyan wasu tsirarun mutane ne ya haddassa matsalar wadda aka kasa magancewa har yanzu a Nijeriya, musamman a yankin arewa.

  • Kokarin CBN Wajen Daga Darajar Naira

Ya ce sanin kowa ne akwai matsalolin tsaro da kasar nan ke fuskanta a halin yanzu, wanda ya fi fice shi ne matsalar ‘yan bindiga da masu garkuwa da mutane da kisan gilla da suka addabi yankin arewa maso yamma. A cewarsa, wadannan matsaloli ko shakka babu suna kara dagula ci gaban kasar nan.

Alhaji Ibrahim ya ce jami’an tsaro sun dade suna kokawa a kan yawaitar miyagun makamai a cikin kasar nan, wadanda muyagun ‘yan siyasa suke amfani da su wajen cimma burikansu da ke jefa dar-dar a zukatan jama’a.

Ya ce matsalolin tsaro suka kara ta’azzara a cikin kasar nan, kuma akwai bukatar masu ruwa da tsaki tun daga kan shugabanni da sarakuna da jami’an taro da su yi wa tukar hanci, domin duk ranar da ‘yan kasa suka fusata hankali zai tashi fiye da wanda aka gani a zanga-zangar Endsas da ta gudana a kudu.

Shugaban gamayyar ya yi kira da shugabanni da su gaggauta sayo kan matsalar tsaro a fadin kasar nan tun kafin lokaci ya kure musu, domin idan tura-ta-kai bango har har talakawa suka fusata, to abubuwa ba za su yi kyau ba.
Ya ce kashi sittin na matsalolin tsoro a kasar nan suna faruwa ne saboda rashin cika alkawura ga jama’a da shugabanni ke yi da rashin adalci da rashin tausayi na shugabanni ga talakawansu, wannan ne ya samar da rashin tagomashi na gwamnati ga jama’a, inda a yanzu an kai lokacin da mulki da shugabanci suka zama abin son zuciya, babu wanda zai iya tabbatar da cewa akasarin wadanda aka zaba su wakilci jama’a na yin hakan kamar yadda ya dace ba tare da son zuciya ba.

Labarai Masu Nasaba

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Daga karshe ya yi kira da shugabanci da su sani duniya ba wurin zama ba ne, kuma duk abin da suka shuka, shi ne za su girba a gobe kiyama. Ya ce idan aka cire son zuciya komai zai kawo karshe a ɓangaren matsalar tsaro.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kokarin CBN Wajen Daga Darajar Naira

Next Post

Kusan Shekara 100 Da Kafa Asibitin Kutare Na Kano, Amma…

Related

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?
Manyan Labarai

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

11 minutes ago
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

24 minutes ago
Tsaro
Labarai

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

2 hours ago
An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki
Labarai

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

4 hours ago
Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi
Labarai

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

4 hours ago
Tsaro
Labarai

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

7 hours ago
Next Post
Kusan Shekara 100 Da Kafa Asibitin Kutare Na Kano, Amma…

Kusan Shekara 100 Da Kafa Asibitin Kutare Na Kano, Amma…

LABARAI MASU NASABA

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
Tsaro

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Xi Jinping Ya Aika Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafuwar Jam’iyyar Zhigong Ta Sin

Xi Jinping Ya Aika Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafuwar Jam’iyyar Zhigong Ta Sin

September 19, 2025
An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

September 19, 2025
Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

September 19, 2025
Tsaro

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

September 19, 2025
Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.