ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 28, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kusan Shekara 100 Da Kafa Asibitin Kutare Na Kano, Amma…

by Sulaiman and Sabo Ahmad
4 years ago
Kutare
  • Har Yanzu Galibin Mutane Ba Su Fahimci Muhimmancinsa Ba
  • AkwaiKarancin Ma’aikata
  • Wasu Makota Na Yi Masa Zagon Kasa
  • ‘Yan Sumoga Sun Addabi Harabarsa, In Ji Daraktansa

LEADERSHIP HAUSA ta yi tattaki zuwa Asibitin Kutare na Bela da ke kan hanyar Gezawa a karamar hukumar Tofa ta Jihar Kano, domin kawo wa masu karatunmu labari a kan halin da asibitin ke ciki, da kuma fahimtar da al’umma irin ayyukan kiwon lafiyar da yake yi domin ‘yan kasa su ci gajiyar asibitin.

Wakilinmu SABO AHMAD KAFIN-MAIYAKI ya zanta da Daraktan Shiyya na hukumar da ke kula da asibitocin Jihar Kano, shiyya ta daya, wadanda suka kunshi Asibitin Kutare na Bela, da Asibitin Zana da na Hakori, ABDULLAHI ISMA’ILA KWALWA. Ga dai yadda tattaunawar tasu ta kasance:

Darakta, barka da warhaka. Masu karatunmu za su so, ka gabatar da kanka.
Sunana Abdullahi Isma’ila Kwalwa. Ni ne Daraktan shiyya na hukumar da ke kula da asibitici a jihar Kano, shiyya ta daya da ke kula da Asibitin kutare na Bela da Asibitin Zana da Asibitin Hakori da kuma wasu asibiti guda uku kanana, wadanda suke kunshi asibitocin shiyyar guda shida.

ADVERTISEMENT

Menene tarihin wannan asibitin kutare na Bela?
An kafa wannan asibiti a shekara ta 1930, lokacin Sarkin Kano, Abdullahi Bayero. An yi niyyar kafa wannan asibitin ne da a garin Sumaila, amma sai aka zo aka yi shi a wannan muhallin da kake ganinsa a halin yanzu, ganin cewa, a wannan gurin zai fi saukin shiga da fita, musamman ga wadanda ke nesa, amma saboda yanayin irin mutane da ke jiyya a wannan asibiti, ya zama an nesanta shi daga cikin al’ummar gari, yadda majiyayyata za su samu walwala ba tare da nuna tsangwama ba daga wasu al’umma. Asibitin Bela asibiti ne da ke da haraba mai fadin gaske. An debi wannan harabar ce, tun a wancan lokacin bisa hasashen duk loacin da aka bukaci fadada shi, za iya fadada shi ba tare da wata matsala ba.
A cikin shekara ta 1975, Gwamnan Jihar Kano Audu Bako a wancan lokacin ya zo ya yanki wani bangare na wannan asibiti, ya sa aka haka dam. Sai dai babban abin takaici shi ne, yadda wasu bata-gari ke neman hana ruwa gudu a wannan asibiti, musamman wasu daga cikin makotan asibitin, ta hanyar karkatar da wasu marasa lafiya zuwa wasu a sibitoci masu zaman kansu, wanda hakan na daga cikin abin da ya zame wan nan asibiti alakakai.
Tun daga wancan lokacin zuwa yanzu, asibitin ya kai kusan kimanin shekara dari da kafa shi, saboda haka, yana da dogon tarihi, tun lokacin Turawan milkin mallaka.
Tun daga wancan lokacin da aka kafa shi, ya ci gaba da samun ci gaba, inda bayan kasancewarsa asibitin kutare ya zama ana karbar haihuwa a cikinsa, an kuma samu dakin gwaje-gwaje da kuma dakin daukar hoto, samar da wadannan ayyuka da ake yi a wannan asibiti, sai aka daga darajarsa ya tashi daga asibitin kutare, ya zama Babban Asibiti. Saboda haka sai ya zama yana samar da lafiya ga yara da mata da sannan kuma ana kwanciya a cikinsa, sannan kuma asibitin na yin ayyukan riga-kafi.
Saboda haka ida aka dubi asibitin a halin yanzu za a iya cewa, ya samu ci gaban da majiyyata ke zuwa daga kowane sashi na kasar nan domin a kula da lafiyarsu, kuma daidai gwarwado suna samun biyan bukata.

Wadanne kakubale wannan asibiti ke fuskanta a halin yanzu?
Babban kalubalen da wannan asibiti ke fuskanta shi ne, karancin ma’aikata, a wannan asibitin muna da bangaren sha-ka-tafi, muna da kwararrun likitoci a bangaren fata, saboda haka, dukkan wani likita da zai tura majiyyaci kan aikin fata asibitin Bela zai tura, saboda muna da kwararrun lilitocin fata, a wannan asibitin, wanda ya sa al’umma daga ko’ina da suke da matsalar da ta shafi fata ke zuwa wannan asibitin.
Wannan ta sa nake ganin indai za a yi maganar babban kalubalen da wannan asibitin ke fuskanta bai wuce na rashin wadatattun ma’aikata ba.
Wani babban kalubale, ko kuma in ce babbar barazar da wannan asibitin ke fuskanta ita ce, har yau mutanen da ke makotaka da wannan asibiti ba su fahimci amfaninsa ba. Kusan shekara dari da kafa wannan asibitin amma har yanzu wasu da yawa daga cikin mutanen wajen ba su fahimci muhimmancin asibitin ba, musamman kan yadda za su bayar da gudummowa wajen ganin ya samu ci gaba, saboda haka ka da su dauka cewa, lallai sai gwamnati ce za ta taimaka wa wannan asibitin al’umma sun a suna da gudummowar da za su bayar.
Wata babbar matsala da wannan asibitin ke fuskanta daga wasu mazauna wannan yanki, shi ne yadda sukan bi sawun mara lafiya, yadda za su kwadaitar da shi ya bar wannan asibitin zuwa wani asibitin mai zaman kansa, yadda za su hada baki inda suka kai shi domin su sanu kudi, daga mara lafiya da kuma asibitin da suka kai majiyyaci.
Karin wani babban kalubalen da wannan asibitin ke fuskanta shi ne na tsaro, yadda wasu masu somoga da sauran wasu masu laifi kan keto ta harabar wannan asibiti, wanda hakan ke zaman wata babbar barazana ga wannan asibitin da kuma majiyyatan da ke cikinsa, musamman a wannan lokaci da ake fuskantar matsalar tsaro, kuma da ma wasu majiyyatan za ka samu baki ne, ba su san yanayin yankin ba, ka ga hakan na iya dagula musu lissafi ta hanyar jefa musu tsoro cikin zukatansu. Shi majiyyaci kullum ana bukatar ya samu kwanciyar hankali ba tashin hankali ba, domin fadawarsa cikin tashin ba zai taimaka masa ba wajen samun lafiyar da ya zo nema ba.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

Yadda Rikice-rikice Ke Ƙara Ta’azzara Talauci A Arewacin Nijeriya —Rahoto

Wane sako kake da shi ga majiyyata da ke wannan Asibiti?
A gaskiya, majiyyata na kokari matuka, ka ga majiyyata kan zo daga nesa, kamar Nijar da Yobe da Maiduguri, kai kusan ko’ina a fadin kasar nan domin neman lafiya, kuma sukan zo ba tare da cewa, sun san wani a wannan gari ba, maganar neman lafiyar ce kawai ke kawo su.
Sai dai babban kiran da zan yi musu shi ne, su kara hakuri, yayin da suka zo wajen neman lafiya, kuma su daure su bi dokokin da likita ya kafa musu, domin su samu warakar da suka zo nema, sannan kuma su yi hankali da wasu mutane da ka iya zuwa wajensu, da niyyar cewa, za su taimake su, su kai su wani asibitin da za a kula da su, cikin gaggawa.

Akwai wani sako da kake da shi musamman ga masu hannu da shuni da ke kusa da kuma na nesa da wannan asibitin?
Babban sakona shi ne, musamman ga masu hannu da shuni, shi ne su yi amfani da damar da Allah ya ba su wajen taimaka wa wannan asibiti wanda dimbin al’umma ke amfana da shi. Domin kuwa da irin wannan gudummowarce wasu asibitoci suka bunkasa, bas a jiran gwamnati, musamman a wannan kasa idan muka lura, za a iya cewa, nauyi ya yi wa gwamnati yawa, saboda haka, akwai bukatar masu hannu da shuni su shiga sahun masu bayar da taimako ga wannan asibiti, mai dimbin tarihin da ya shafe kusan sheka dari yana gudanar da ayyukan lafiya.
Wane sako kake da shi ga al’ummar wannan yanki da wannan asibiti ke ciki, sakona shi ne su kara jin tsoron Allah, su tabbatar sun bayar da gudummowar gina wannan asibitin ba rusa shi ba, wannan kuma zai raimaka wajen su kansu mazauana yankin su kara samun ci gaba.
Ga gwamnati kuma, za mu iya cewa, kokarin da take wajen inganta wannan asibi na taimaka wa majiyyata wajen samun kulawar da ta kamata ga marasa lafiyar da suka zo nema daga mesa da kusa a dukkan fadin kasar nan.

Kutare
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara
  • Sulaiman
    Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna
  • Sulaiman
    Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki
  • Sulaiman
    Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh
Kutare
Sabo Ahmad
+ posts Bio
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    An Gurfanar Da Mutum 3 Bisa Laifin Lakada Wa Wani Duka Har Lahira
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    Dalilin Da Ya Sa Kotu Ta Tasa Keyar Dakta Idris Dutsen Tanshi Zuwa Gidan Yari
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    Uwa Ta Mutu A Kokarin Raba Fada Tsakanin ‘Ya’yanta A Abuja
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    ’Yan Fashi Sun Yi Shigar Injiniyoyi, Sun Saci Manyan Na’urorin Sadarwa

MASU ALAKA

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
An Kashe Mutane Da Dama Da Kone Gidajensu A Wani Hari Da Aka Kai Benuwai
Rahotonni

Yadda Rikice-rikice Ke Ƙara Ta’azzara Talauci A Arewacin Nijeriya —Rahoto

June 26, 2026
Noma
Rahotonni

Ƙa’idojin Gudanar Da Biyan Kuɗi Nan Take Domin Kare Kai Daga Zamba

June 26, 2026
Next Post
Kamata Ya Yi Dalibai Su Maka Kungiyar ASUU A Kotu Kan Bata Musu Lokaci—Adamu Adamu

Kamata Ya Yi Dalibai Su Maka Kungiyar ASUU A Kotu Kan Bata Musu Lokaci—Adamu Adamu

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

June 28, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

June 28, 2026
Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

June 28, 2026
Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

June 28, 2026
Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh

June 28, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

El-Rufai Ya Shafe Fiye Da Kwanaki 125 A Garƙame

June 28, 2026
Ghana Ta Soke Lasisin Mallakar Bindiga Da Aka Bai Wa Fararen Hula A Baya

Ghana Ta Soke Lasisin Mallakar Bindiga Da Aka Bai Wa Fararen Hula A Baya

June 28, 2026
Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

June 27, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Iran Ta Jaddada Cewa Ba Ta Da Wani Shiri Na Bada Damar Binciken Wuraren Nukiliyarta

June 27, 2026
Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

June 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.