• English
  • Business News
Monday, October 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Suyar Sallah: Sojojin Sama Sun Soya Ƴan Ta’adda 80 A Katsina

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Suyar Sallah: Sojojin Sama Sun Soya Ƴan Ta’adda 80 A Katsina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar Sojin saman Nijeriya ta tabbatar da kashe ‘yan ta’adda sama da 80 tare da lalata babura 45 a wani harin da ta kai ta sama a ƙauyen Gidan Kare da ke jihar Katsina.

An kai harin ne a ranar 15 ga watan Yunin 2024, bayan wasu bayanan sirri sun nuna cewa sama da ‘yan ta’adda 100 ne ke kona gidaje tare da shirin ƙara kai hare-hare a wasu ƙauyukan da ke kusa.

An hango ‘yan ta’addan suna taruwa a wani wuri da ke kusa da ƙauyen Gidan Kare da kuma sansanin Kuka Shidda kafin rundunar Sojojin ta NAF ta far musu, lamarin da ya kawo ƙarshen ayyukansu.

  • Sojoji Na Kan Bakarsu Na Tabbatar Da Tsaron Kasa – Shugaban Tsaro
  • An Tafka Gumurzu, Sojoji Sun Kashe Ƴan Boko Haram Da Yawa, Wasu Sun Miƙa Wuya

Iya Mashal Edward Gabkwet ya bayyana cewa ‘yan ta’addan na da alaƙa da manyan ƴan ta’adda irinsu Yusuf Yellow da Rabe Imani.

Hare-haren ta sama, wanda aka ba da izini bayan an kiyayewa kuskure, ya samu gagarumar nasarar kawar da barazanar ƴan ta’addan daga yankin.

Labarai Masu Nasaba

Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

Zaratan Sojojin Saman Nijeriya
Zaratan Sojojin Saman Nijeriya

Wannan farmakin dai na daga cikin ƙoƙarin da ake yi na kakkabe hanyoyin sadarwar ‘yan ta’adda a yankin da kuma hana kai hare-hare a nan gaba.

Shugaban hafsan sojin sama, Iya Mashal Hassan Abubakar, ya yabawa rundunar Sojin sama da sauran jami’an tsaro bisa haɗin kan da suke yi wajen yaƙi da ta’addanci a yankin Arewa maso yamma.

A ziyarar da ya kai sansanin ‘Forward Operating Base’ mai lamba 213 da ke Katsina, ya jaddada muhimmancin ci gaba da sadaukarwar da suke da shi, ya kuma ƙaddamar da sabbin na’urori na filayen jiragen sama domin inganta ayyukansu.

Wannan yunƙurin wani ɓangare ne na dabarun tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali na dogon lokaci a yankin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArmyBanditsKatsinaSojojiTerrorist
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Farfadowa Tare Da Nuna Kyakkyawar Yanayi A Watan Mayu

Next Post

Binciken CGTN: An Yi Kira Ga Kasashe Masu Ci Gaba Da Su Kara Daukar Nauyin Da Ya Dace Kan Matsanancin Yanayi Da Ake Samu A Kai A Kai

Related

Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu
Manyan Labarai

Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

19 minutes ago
Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara
Tsaro

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

9 hours ago
Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa
Labarai

Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

9 hours ago
Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya
Labarai

Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

10 hours ago
NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC
Labarai

NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

11 hours ago
Ranar Malamai ta Duniya: Ƙungiyar NUT Ta Koka Kan Ƙarancin Malamai 194,000 A Nijeriya
Labarai

Ranar Malamai ta Duniya: Ƙungiyar NUT Ta Koka Kan Ƙarancin Malamai 194,000 A Nijeriya

14 hours ago
Next Post
Binciken CGTN: An Yi Kira Ga Kasashe Masu Ci Gaba Da Su Kara Daukar Nauyin Da Ya Dace Kan Matsanancin Yanayi Da Ake Samu A Kai A Kai

Binciken CGTN: An Yi Kira Ga Kasashe Masu Ci Gaba Da Su Kara Daukar Nauyin Da Ya Dace Kan Matsanancin Yanayi Da Ake Samu A Kai A Kai

LABARAI MASU NASABA

Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

October 6, 2025
Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

October 5, 2025
Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

October 5, 2025
CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

October 5, 2025
Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

October 5, 2025
Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

October 5, 2025
NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

October 5, 2025
Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

October 5, 2025
Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

October 5, 2025
Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

October 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.