• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ta Ina Talakawa Za Su Mori Rage Farashin Simintin BUA?

by Bello Hamza
2 years ago
in Labarai
0
BUA
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamar yadda aka sani, kamfanin siminti na BUA karkashin jagorancin Alhaji Abdussamad Rabiu ya sanar da cewa, nan gaba kadan zai rage farashin siminti a fadin kasar daga naira 5,500 a kan kowanne buhu zuwa Naira 3,000. Ya ce, sun yanke wannan shawarar ne don yin haka tamkar nuna goyon bayansu ga kudurin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu na samar da isssun gidaje ga al’umma Nijeriya da kuma hankoron ganin an samar da ayyukan yi ga dinbin matasanmu.

Tabbas wannan shirin zai taikama wa rayuwwar talakan Nijeriya, don samar da siminti mai sauki zai zaburar da harkar kwangila na gine-gine a fadin tarayya Nijeriya abin da kuma zai kai ga daukar masu kananan sana’o’i da leburori da dama aiki.

  • An Gabatar Da Sanarwar Taron Kula Da Harkokin Masana’antu Da Kasuwanci Bisa Doka
  • Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Sabbin Shirye-shiryen Inganta Tsaro A Jihar Kaduna

Babu shakka in har leburori da birkila, da masu walda da fulamba da sauran wadanda suke gudanar da sana’ar su da ta shafi bangaren gine-gine suka samu abin yi, al’umma da suka shafe su za su samu abinci mutane za su samu karin walwala.

Sai dai tambayar da mutane da dama suke yi, shi ne wai shin yaushe za a fara cin gajiyar wannan rage farashin? Shugaban kamfanin BUA, Alhaji Abudussamad Rabiu ya ce, wannan Shirin ya danganta ne ga shirinnsu na bude wasu sabbin kamfanoni biyu da suke sa ran za su rinka samar da tan miliyan 3 na siminti a duk mshekara wanda suke sa ran za a kamala aikin ginawa nan zuwa karshen shekara.

Sabbin kamfanonin guda biyu in har suka fara aikii za su kara yawan simintin da BUA ke samarwa zuwa tan Miliyan 17 a duk shekara wanda hakan zai mayar da kamfanin mafi girma a bangaren samar da siminti a fadin Afirka gaba daya. Shugaban kamfanin ya ce, suna sa ran cimma wanna ne saboda yadda suke samar da kayan hada simininti a cikin gida.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Na Kashe Naira Miliyan 4.3 A Kullum Don Ciyar Da Wadanda Ke Jiran Hukuncin Kisa

2027: Gangamin ‘Yan Adawa Ya Sa APC Fafutukar Neman Mafita

“Kashi 80 na kayan da muke hada siminti da su muna samu ne daga cikin gida, a kan haka muke son tallafa wa gwamnati wajen tabbatar da ganin an dawo da farashin siminti zuwa farashin da ya dace da talaka.” In ji shi.

Abdussamad Rabiu ya kuma bayyana cewa, ana sa ran shugaban kasa Tinubu zai kaddamar da sabbin kamfanin nan gaba a cikin wannan shekarar ta yadda abin da muke samarwa zai kai tan miliyan 17 a duk shekara.

Masu sharhi a kan harkokin yau da kullum sun nuna jin dadinsu a kan wannan matakin suna mai cewa, yin hakan zai zaburar da tattalin arzikin kasa, musamman a bangaren gine-gine na kamfanoni da mutane daidaiku.
Wannan ragin kuma zai taimaki al’umma musamman masu gidaje da masu haya don zai kai ga rage kudin haya a nan gaba.
Kotu Da “yansanda


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BUADangote
ShareTweetSendShare
Previous Post

Matakan Fara Sana’ar Hakar Ma’adanai Bisa Doka A Nijeriya

Next Post

Ɗaliban Musawa Da Matazu Za Su Amfana Da Tallafin Karatun Naira Miliyan 32,500 A Katsina

Related

Fyade
Rahotonni

Nijeriya Na Kashe Naira Miliyan 4.3 A Kullum Don Ciyar Da Wadanda Ke Jiran Hukuncin Kisa

2 hours ago
APC
Manyan Labarai

2027: Gangamin ‘Yan Adawa Ya Sa APC Fafutukar Neman Mafita

3 hours ago
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya
Labarai

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

14 hours ago
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano
Labarai

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

15 hours ago
Kasar Sin Ta Nuna Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Nijeriya Buhari
Labarai

Za A Dinga Tunawa Da Buhari A Matsayin Waliyyi A Siyasar Nijeriya —Dakta Zangina

16 hours ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Nada Ɗan Babangida A Matsayin Shugaban Bankin Manoma

16 hours ago
Next Post
Ɗaliban Musawa Da Matazu Za Su Amfana Da Tallafin Karatun Naira Miliyan 32,500 A Katsina

Ɗaliban Musawa Da Matazu Za Su Amfana Da Tallafin Karatun Naira Miliyan 32,500 A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Shettima

Nijeriya Za Ta Rika Samun Naira Tiriliyan Uku A Aikin Tatsar Rogo Duk Shekara – Kashim

July 19, 2025
Fyade

Nijeriya Na Kashe Naira Miliyan 4.3 A Kullum Don Ciyar Da Wadanda Ke Jiran Hukuncin Kisa

July 19, 2025
APC

2027: Gangamin ‘Yan Adawa Ya Sa APC Fafutukar Neman Mafita

July 19, 2025
Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.