• English
  • Business News
Monday, June 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ta’addanci Na Haifar Da Illa Musamman Ga Mata — Amina Mohammed

by Sadiq
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Ta’addanci Na Haifar Da Illa Musamman Ga Mata — Amina Mohammed
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mataimakiyar Sakatare Janar ta Majalisar Dinkin Duniya, Amina Mohammed, ta jaddada muhimmancin magance matsalolin ta’addanci da tallafa wa al’ummomin da abin ya shafa a fadin Afirka.

Mataimakiyar ta bayyana haka ne a yayin wani taro na yaki da ta’addanci da aka gudanar a ranar Litinin, a Abuja.

  • PSG Na Neman Dauko Lamine Yamal Daga Barcelona A Kan Yuro Miliyan 200
  • EFCC Ta Sake Maka Emefiele A Kotu Kan Wasu Sabbin Tuhume-tuhume 4

Ofishin Mai Ba Da Shawara kan Harkokin Tsaro (ONSA) tare da hadin gwiwar ofishin yaki da ta’addanci na Majalisar Dinkin Duniya (UNOCT) ne, suka shirya taron.

Taron da aka yi wa taken ‘Karfafa Hadin Gwiwar Yanki Da Ci Gaban Cibiyoyi Don Tunkarar Barazanar Ta’addanci a Afirka’.

Amina ta kara jaddada illar ta’addanci da munanan illolin da yake haifarwa ga al’umma, musamman mata da ‘yan mata wadanda galibi su ne ke fuskantar cin zarafin ta’addanci.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

Bugu da kari, ta yaba wa Nijeriya bisa kiran taron kolin don magance matsalolin mata, masu rauni, da wadanda ta’addanci ya shafa.

“Dole ne mu samar da ingantattun dabaru da za su magance wadannan kalubale, tare da mayar da hankali kan halin da mata da ‘yan mata ke ciki wadanda rashin tsaro ya shafa,” in ji ta.

Da ta ke bayyana muhimmancin saka hannun jari ga matasa, Amina ta bukaci kasashen Afirka da su samar da yanayi mai kyau don ci gabansu da wadata.

Ta kara da cewa muhimmancin taron ya wuce Nijeriya, inda ta yi kira da a yi kokarin hadin gwiwa daga kasashen Afirka a fadin nahiyar, ciki har da Ghana da Togo, domin samun ci gaba wajen yakar ta’addanci da kuma tallafa wa al’ummar da abin ya shafa.

Ta kuma bayyana takaicinta game da yadda ake yin watsi da al’amuran mata da ‘yan mata a manyan tarukan duniya.

“A manyan tarukan da shugabannin kasashen duniya ke tattaunawa, an mayar da hankali ne bisa karfafa gwiwar matasa da matakan yaki da ta’addanci, tare da kawar da matsalolin da suka shafi mata.

“Sai dai a yanzu, abin farin ciki ne ganin yadda al’amuran mata ke samun karbuwa a irin wadannan dandali,” in ji ta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Amina MohammedMajalisar Dinkin DuniyaMataTa'addanciTaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

PSG Na Neman Dauko Lamine Yamal Daga Barcelona A Kan Yuro Miliyan 200

Next Post

Saudiyya Ta Raba Dabino Ga Makarantu, Gidajen Marayu Da Asibitoci A Kano

Related

Gwamnan kano
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

18 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

1 day ago
Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa

2 days ago
Mutane 21 Sun Mutu A Tawagar Ƴan Wasannin Kano A Hatsarin Mota
Manyan Labarai

Mutane 21 Sun Mutu A Tawagar Ƴan Wasannin Kano A Hatsarin Mota

2 days ago
Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas

3 days ago
Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar Da Zaɓen Ƙananan Hukumomin Kano
Manyan Labarai

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar Da Zaɓen Ƙananan Hukumomin Kano

3 days ago
Next Post
Saudiyya Ta Raba Dabino Ga Makarantu, Gidajen Marayu Da Asibitoci A Kano

Saudiyya Ta Raba Dabino Ga Makarantu, Gidajen Marayu Da Asibitoci A Kano

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin

Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin

June 1, 2025
Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa

Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa

June 1, 2025
Ranar Yara Ta Duniya: Yadda Shugaba Xi Ya Kasance Tare Da Yara

Ranar Yara Ta Duniya: Yadda Shugaba Xi Ya Kasance Tare Da Yara

June 1, 2025
Sin Na Matukar Adawa Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka

Sin Na Matukar Adawa Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka

June 1, 2025
Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

June 1, 2025
Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

June 1, 2025
Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

June 1, 2025
bakin wake

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

June 1, 2025
‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

June 1, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

June 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.