• English
  • Business News
Wednesday, August 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ta’addanci Na Haifar Da Illa Musamman Ga Mata — Amina Mohammed

by Sadiq
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Ta’addanci Na Haifar Da Illa Musamman Ga Mata — Amina Mohammed
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mataimakiyar Sakatare Janar ta Majalisar Dinkin Duniya, Amina Mohammed, ta jaddada muhimmancin magance matsalolin ta’addanci da tallafa wa al’ummomin da abin ya shafa a fadin Afirka.

Mataimakiyar ta bayyana haka ne a yayin wani taro na yaki da ta’addanci da aka gudanar a ranar Litinin, a Abuja.

  • PSG Na Neman Dauko Lamine Yamal Daga Barcelona A Kan Yuro Miliyan 200
  • EFCC Ta Sake Maka Emefiele A Kotu Kan Wasu Sabbin Tuhume-tuhume 4

Ofishin Mai Ba Da Shawara kan Harkokin Tsaro (ONSA) tare da hadin gwiwar ofishin yaki da ta’addanci na Majalisar Dinkin Duniya (UNOCT) ne, suka shirya taron.

Taron da aka yi wa taken ‘Karfafa Hadin Gwiwar Yanki Da Ci Gaban Cibiyoyi Don Tunkarar Barazanar Ta’addanci a Afirka’.

Amina ta kara jaddada illar ta’addanci da munanan illolin da yake haifarwa ga al’umma, musamman mata da ‘yan mata wadanda galibi su ne ke fuskantar cin zarafin ta’addanci.

Labarai Masu Nasaba

Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N820 Kan Kowace Lita

Bugu da kari, ta yaba wa Nijeriya bisa kiran taron kolin don magance matsalolin mata, masu rauni, da wadanda ta’addanci ya shafa.

“Dole ne mu samar da ingantattun dabaru da za su magance wadannan kalubale, tare da mayar da hankali kan halin da mata da ‘yan mata ke ciki wadanda rashin tsaro ya shafa,” in ji ta.

Da ta ke bayyana muhimmancin saka hannun jari ga matasa, Amina ta bukaci kasashen Afirka da su samar da yanayi mai kyau don ci gabansu da wadata.

Ta kara da cewa muhimmancin taron ya wuce Nijeriya, inda ta yi kira da a yi kokarin hadin gwiwa daga kasashen Afirka a fadin nahiyar, ciki har da Ghana da Togo, domin samun ci gaba wajen yakar ta’addanci da kuma tallafa wa al’ummar da abin ya shafa.

Ta kuma bayyana takaicinta game da yadda ake yin watsi da al’amuran mata da ‘yan mata a manyan tarukan duniya.

“A manyan tarukan da shugabannin kasashen duniya ke tattaunawa, an mayar da hankali ne bisa karfafa gwiwar matasa da matakan yaki da ta’addanci, tare da kawar da matsalolin da suka shafi mata.

“Sai dai a yanzu, abin farin ciki ne ganin yadda al’amuran mata ke samun karbuwa a irin wadannan dandali,” in ji ta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Amina MohammedMajalisar Dinkin DuniyaMataTa'addanciTaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

PSG Na Neman Dauko Lamine Yamal Daga Barcelona A Kan Yuro Miliyan 200

Next Post

Saudiyya Ta Raba Dabino Ga Makarantu, Gidajen Marayu Da Asibitoci A Kano

Related

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi
Manyan Labarai

Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello

16 minutes ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N820 Kan Kowace Lita

1 hour ago
Kano
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Bayar Da Kwangilar Hanyoyi 17 Akan Naira Biliyan 40.8

15 hours ago
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi
Manyan Labarai

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

18 hours ago
An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami
Manyan Labarai

An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami

20 hours ago
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

Jagora A ADC Ya Ƙaryata Zargin Atiku Ya Kankane Komai A Jam’iyyar

21 hours ago
Next Post
Saudiyya Ta Raba Dabino Ga Makarantu, Gidajen Marayu Da Asibitoci A Kano

Saudiyya Ta Raba Dabino Ga Makarantu, Gidajen Marayu Da Asibitoci A Kano

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello

August 13, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N820 Kan Kowace Lita

August 13, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi

August 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

August 12, 2025
EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

August 12, 2025
Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

August 12, 2025
Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

August 12, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci Sun Kashe Wani Mutum Da Jikkata Wasu Da Dama A Sokoto

August 12, 2025
Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

August 12, 2025
Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 

Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 

August 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.