• English
  • Business News
Wednesday, June 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tabbas Sin Za Ta Ci Gaba Da Jan Zarenta A 2025

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Tabbas Sin Za Ta Ci Gaba Da Jan Zarenta A 2025
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Allah ya kawo mu shekara ta 2025, inda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi wa ’yan kasar jawabi mai ratsa zuciya, kuma mai cike da karsashi na baiwa Sinawa kwarin gwiwa da gamsuwa a kan matsayin da kasar ta kai a yau.

A cikin jawabin nasa, shugaba Xi Jinping ya tabo batutuwa masu muhimmanci da suka hada da tattalin arziki, aikin gona, kimiyya da fasaha, al’adu, zamantakewa tsakanin al’ummar kasar Sin da kuma matsayin Sin a matsayin kasa daya.

  • Ɗan Wasan Super Eagles, Sadiq, Zai Koma Valencia Aro
  • Daga Karshe, Yahaya Bello Ya Fada Hannun EFCC

Alal hakika, idan aka lura da wannan jawabi na Mr. Xi, za’a fahimci cewa ya yi wa kansa da daukacin Sinawa adalci. Domin kuwa ko mutum baya kaunar Allah, dole ne ya yarda cewa tattalin arzikin kasar Sin ya yi matukar bunkasa. Abin lura a nan shi ne, yawancin kasashe ba su yi la’akari da abin da bunkasuwar tattalin arziki ke haifarwa ga muhalli, musamman ta gurbata muhalli da yanayi. Amma abin burgewa a nan dangane da irin bunkasuwar tattalin arzikin da kasar Sin ta samu mai tsabta ne, ba mai gurbata mahahalli ba, sabanin irin yadda wasu kasashen ke zub da dagwalon masana’antu a cikin teku, abin da ke illa ga halittun ruwa, ko kuma fitar da hayaki mai gurbata iska dake illa ga bil adam.

Kada a manta cewa kasar Sin tana kan gaba ta fannin kera motoci masu aiki da wutar lantarki, a cikin shekara ta 2024 kadai, sama da motoci masu aiki da lantarki miliyan goma ne aka kera a kasar Sin. Bugu da kari ita kanta wutar lantarki mai tsabta ce, domin kuwa akasarinta daga hasken rana da karfin iska da ma sauran nau’o’in makamashi masu tsabta ake samunta.

Mu waiwaya bangaren kimiyya da fasaha, kasar Sin ta samu gagarumin ci gaba ta fannin fasahar kwaikwayon tunanin dan Adam (AI) da kuma fasahar sadarwa. Sa’an nan, a karo na farko na’urar bincike ta Chang’e 6 ta dauko samfura daga bangaren bayan duniyar wata, kana babban jirgin ruwan binciken teku na Mengxiang ya gudanar da bincike a sashen teku mai zurfi.

Labarai Masu Nasaba

Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

Idan muka koma bangaren noma kuwa, yau an wayi gari kusan daukacin abincin da Sinawa ke ci, a cikin kasar Sin ake noma shi. A shekarar 2024, adadin yawan hatsin da aka noma a kasar ya kai sama da tan miliyan 700, ba’a ma maganar kayan lambu da sauran nau’ikan ’ya’yan itace. Harkar noma dai ta yi matukar tasiri wajen fitar da mazauna yankunan karkara daga cikin kangin talauci.

Dangantaka tsakanin Sin da sauran kasashen duniya kuwa sai hamdala. Idan ba’a manta ba, a cikin shekarar da ta gabata, Sin ta tara shugabannin kasashen Afirka a birnin Beijing, domin gudanar da taron dandalin hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka. Taron dai ya samu gagarumar nasara, ba domin komai ba, sai don yadda shugabannin na Afirka suka fahimci cewa kasar Sin ba ta da wata boyayyar manufa, illa iyaka kawai domin kowa ya amfana a kuma ci moriyar juna.

Daga karshe, shugaba Xi Jinping ya kara jaddada matsayin kasarsa a kan batutuwan da suka shafi Macao, Hong Kong da kuma Taiwan, a matsayin kasa daya mai bin tsarin mulki biyu. A bayyane take kan irin ci gaban da Macao ta samu tun lokacin dawowarsa karkashin mulkin kasar Sin shekaru 25 da suka gabata. Wannan lamari ya kara kunyata masu kulla makircin ballewar Taiwan daga kasar.

 

 

 

 

 

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Fintiri Ya Nada Sabbin Sarakuna 7 A Jihar Adamawa

Next Post

Sin Ta Cimma Burikanta Na Raya Tattalin Arziki Da Al’Umma a Shekarar 2024

Related

Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana
Daga Birnin Sin

Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

36 minutes ago
Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 
Daga Birnin Sin

Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

2 hours ago
Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

3 hours ago
Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya
Daga Birnin Sin

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

21 hours ago
Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

22 hours ago
Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 
Daga Birnin Sin

Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

22 hours ago
Next Post
Sin Ta Cimma Burikanta Na Raya Tattalin Arziki Da Al’Umma a Shekarar 2024

Sin Ta Cimma Burikanta Na Raya Tattalin Arziki Da Al’Umma a Shekarar 2024

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

June 4, 2025
Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

June 4, 2025
Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

June 4, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

June 4, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

June 4, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 

June 4, 2025
Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

June 4, 2025
DSS

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

June 4, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 4, 2025
katsina

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Hadin Gwiwa Da ‘Yan Kasuwa Domin Cigaban Jihar

June 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.