ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tabbas Sin Za Ta Ci Gaba Da Jan Zarenta A 2025

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Sin

Allah ya kawo mu shekara ta 2025, inda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi wa ’yan kasar jawabi mai ratsa zuciya, kuma mai cike da karsashi na baiwa Sinawa kwarin gwiwa da gamsuwa a kan matsayin da kasar ta kai a yau.

A cikin jawabin nasa, shugaba Xi Jinping ya tabo batutuwa masu muhimmanci da suka hada da tattalin arziki, aikin gona, kimiyya da fasaha, al’adu, zamantakewa tsakanin al’ummar kasar Sin da kuma matsayin Sin a matsayin kasa daya.

  • Ɗan Wasan Super Eagles, Sadiq, Zai Koma Valencia Aro
  • Daga Karshe, Yahaya Bello Ya Fada Hannun EFCC

Alal hakika, idan aka lura da wannan jawabi na Mr. Xi, za’a fahimci cewa ya yi wa kansa da daukacin Sinawa adalci. Domin kuwa ko mutum baya kaunar Allah, dole ne ya yarda cewa tattalin arzikin kasar Sin ya yi matukar bunkasa. Abin lura a nan shi ne, yawancin kasashe ba su yi la’akari da abin da bunkasuwar tattalin arziki ke haifarwa ga muhalli, musamman ta gurbata muhalli da yanayi. Amma abin burgewa a nan dangane da irin bunkasuwar tattalin arzikin da kasar Sin ta samu mai tsabta ne, ba mai gurbata mahahalli ba, sabanin irin yadda wasu kasashen ke zub da dagwalon masana’antu a cikin teku, abin da ke illa ga halittun ruwa, ko kuma fitar da hayaki mai gurbata iska dake illa ga bil adam.

ADVERTISEMENT

Kada a manta cewa kasar Sin tana kan gaba ta fannin kera motoci masu aiki da wutar lantarki, a cikin shekara ta 2024 kadai, sama da motoci masu aiki da lantarki miliyan goma ne aka kera a kasar Sin. Bugu da kari ita kanta wutar lantarki mai tsabta ce, domin kuwa akasarinta daga hasken rana da karfin iska da ma sauran nau’o’in makamashi masu tsabta ake samunta.

Mu waiwaya bangaren kimiyya da fasaha, kasar Sin ta samu gagarumin ci gaba ta fannin fasahar kwaikwayon tunanin dan Adam (AI) da kuma fasahar sadarwa. Sa’an nan, a karo na farko na’urar bincike ta Chang’e 6 ta dauko samfura daga bangaren bayan duniyar wata, kana babban jirgin ruwan binciken teku na Mengxiang ya gudanar da bincike a sashen teku mai zurfi.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Idan muka koma bangaren noma kuwa, yau an wayi gari kusan daukacin abincin da Sinawa ke ci, a cikin kasar Sin ake noma shi. A shekarar 2024, adadin yawan hatsin da aka noma a kasar ya kai sama da tan miliyan 700, ba’a ma maganar kayan lambu da sauran nau’ikan ’ya’yan itace. Harkar noma dai ta yi matukar tasiri wajen fitar da mazauna yankunan karkara daga cikin kangin talauci.

Dangantaka tsakanin Sin da sauran kasashen duniya kuwa sai hamdala. Idan ba’a manta ba, a cikin shekarar da ta gabata, Sin ta tara shugabannin kasashen Afirka a birnin Beijing, domin gudanar da taron dandalin hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka. Taron dai ya samu gagarumar nasara, ba domin komai ba, sai don yadda shugabannin na Afirka suka fahimci cewa kasar Sin ba ta da wata boyayyar manufa, illa iyaka kawai domin kowa ya amfana a kuma ci moriyar juna.

Daga karshe, shugaba Xi Jinping ya kara jaddada matsayin kasarsa a kan batutuwan da suka shafi Macao, Hong Kong da kuma Taiwan, a matsayin kasa daya mai bin tsarin mulki biyu. A bayyane take kan irin ci gaban da Macao ta samu tun lokacin dawowarsa karkashin mulkin kasar Sin shekaru 25 da suka gabata. Wannan lamari ya kara kunyata masu kulla makircin ballewar Taiwan daga kasar.

 

 

 

 

 

 

 

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Sin Ta Cimma Burikanta Na Raya Tattalin Arziki Da Al’Umma a Shekarar 2024

Sin Ta Cimma Burikanta Na Raya Tattalin Arziki Da Al’Umma a Shekarar 2024

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.