ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tabbas Sin Za Ta Ci Gaba Da Jan Zarenta A 2025

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Sin

Allah ya kawo mu shekara ta 2025, inda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi wa ’yan kasar jawabi mai ratsa zuciya, kuma mai cike da karsashi na baiwa Sinawa kwarin gwiwa da gamsuwa a kan matsayin da kasar ta kai a yau.

A cikin jawabin nasa, shugaba Xi Jinping ya tabo batutuwa masu muhimmanci da suka hada da tattalin arziki, aikin gona, kimiyya da fasaha, al’adu, zamantakewa tsakanin al’ummar kasar Sin da kuma matsayin Sin a matsayin kasa daya.

  • Ɗan Wasan Super Eagles, Sadiq, Zai Koma Valencia Aro
  • Daga Karshe, Yahaya Bello Ya Fada Hannun EFCC

Alal hakika, idan aka lura da wannan jawabi na Mr. Xi, za’a fahimci cewa ya yi wa kansa da daukacin Sinawa adalci. Domin kuwa ko mutum baya kaunar Allah, dole ne ya yarda cewa tattalin arzikin kasar Sin ya yi matukar bunkasa. Abin lura a nan shi ne, yawancin kasashe ba su yi la’akari da abin da bunkasuwar tattalin arziki ke haifarwa ga muhalli, musamman ta gurbata muhalli da yanayi. Amma abin burgewa a nan dangane da irin bunkasuwar tattalin arzikin da kasar Sin ta samu mai tsabta ne, ba mai gurbata mahahalli ba, sabanin irin yadda wasu kasashen ke zub da dagwalon masana’antu a cikin teku, abin da ke illa ga halittun ruwa, ko kuma fitar da hayaki mai gurbata iska dake illa ga bil adam.

ADVERTISEMENT

Kada a manta cewa kasar Sin tana kan gaba ta fannin kera motoci masu aiki da wutar lantarki, a cikin shekara ta 2024 kadai, sama da motoci masu aiki da lantarki miliyan goma ne aka kera a kasar Sin. Bugu da kari ita kanta wutar lantarki mai tsabta ce, domin kuwa akasarinta daga hasken rana da karfin iska da ma sauran nau’o’in makamashi masu tsabta ake samunta.

Mu waiwaya bangaren kimiyya da fasaha, kasar Sin ta samu gagarumin ci gaba ta fannin fasahar kwaikwayon tunanin dan Adam (AI) da kuma fasahar sadarwa. Sa’an nan, a karo na farko na’urar bincike ta Chang’e 6 ta dauko samfura daga bangaren bayan duniyar wata, kana babban jirgin ruwan binciken teku na Mengxiang ya gudanar da bincike a sashen teku mai zurfi.

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Idan muka koma bangaren noma kuwa, yau an wayi gari kusan daukacin abincin da Sinawa ke ci, a cikin kasar Sin ake noma shi. A shekarar 2024, adadin yawan hatsin da aka noma a kasar ya kai sama da tan miliyan 700, ba’a ma maganar kayan lambu da sauran nau’ikan ’ya’yan itace. Harkar noma dai ta yi matukar tasiri wajen fitar da mazauna yankunan karkara daga cikin kangin talauci.

Dangantaka tsakanin Sin da sauran kasashen duniya kuwa sai hamdala. Idan ba’a manta ba, a cikin shekarar da ta gabata, Sin ta tara shugabannin kasashen Afirka a birnin Beijing, domin gudanar da taron dandalin hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka. Taron dai ya samu gagarumar nasara, ba domin komai ba, sai don yadda shugabannin na Afirka suka fahimci cewa kasar Sin ba ta da wata boyayyar manufa, illa iyaka kawai domin kowa ya amfana a kuma ci moriyar juna.

Daga karshe, shugaba Xi Jinping ya kara jaddada matsayin kasarsa a kan batutuwan da suka shafi Macao, Hong Kong da kuma Taiwan, a matsayin kasa daya mai bin tsarin mulki biyu. A bayyane take kan irin ci gaban da Macao ta samu tun lokacin dawowarsa karkashin mulkin kasar Sin shekaru 25 da suka gabata. Wannan lamari ya kara kunyata masu kulla makircin ballewar Taiwan daga kasar.

 

 

 

 

 

 

 

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
  • Sulaiman
    Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

MASU ALAKA

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Next Post
Sin Ta Cimma Burikanta Na Raya Tattalin Arziki Da Al’Umma a Shekarar 2024

Sin Ta Cimma Burikanta Na Raya Tattalin Arziki Da Al’Umma a Shekarar 2024

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.