• English
  • Business News
Thursday, July 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tagomashin Da CBN Ya Samar Wajen Bunkasa Kanana Da Matsakaitan Sana’o’i

by Abubakar Abba
3 years ago
in Labaran Kasuwanci
0
Noma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bisa ga mayar da hankalin da Gwamnan Babban Bankin Nijeriya CBN Godwin Emefele ya yi a karkashin shugabancin bankin, ta hanyar kirkiro da tsare-tsare, musamman don ya karfafa wa masu kanana da matsakaitan sana’o’i (SMEs) a daukacin fadin kasar nan, ganin cewa fannin na (SMEs) na bayar da gagarumar gudunmawa wajen taimakawa da kara bunkasa tattalin arziki, bankin ya kirkiro da tsarin zuba kudade ga fannin kanana da matsakaitan sana’o’i.

Har ila yau, CBN a bisa duba na musamman a fannonin bayanai da sadarwa ta kimiyya (ICT), CBN ya kara bunkasa fannin don ya tafi kafada da kafa da na fadin duniya, musamman don a kara karfafa yin kere-kere da kara wa matasa kwarin gwiwar rungumar koyon sana’o’i.

  • Nasarar Tsarin CBN Na Samar Da Kudaden Habaka Tattalin Arzikin Nijeriya

Ganin cewa, Babban Bankin Nijeriya CBN na tafiya ne da zamani ya kuma yi amfani da fasahar zamani da ya kirkiro domin ganin ya habaka fannin na kanana da matsakaitan sana’oi SMEs.

Hatta a daukacin fadin duniya, kasashen da suka ci gaba irin wannan tsarin ne suka runguma domin su kara bunkasa tattalin arzikinsu.

CBN a karkashin wannan shirin samar da daukin kudade a fannin na kanana da matsakaitan sana’oi, ya yi namiji kokarin wajen samar da daukin kudade ga SMEs, musamman domin a kara bunkasa fannin don a kara habaka tattalin arzikin Nijeriya, musamman fannin aikin noma da kere-kere.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Kuratan Sojoji 1,196 Aka Yaye A Makarantar Horar Da Sojoji Ta Zariya

Alal misali, a bangaren fannin aikin noma, Emefele ya mayar da hankali a kanan da matsakaitan sana’oi ta hanyar shirin aikin noma na na ba da rance ‘Anchor Borrowers’ inda wannna shirin ya kutsa cikin daukacin fannonin aikin noma na kasar nan.

Har ila yau CBN ya samar da damarmaki ga wadanda za su amfana, CBN ya zuba a kai dauki kai tsaye don a karfafa kanana da matsakaitan sana’oi a cikin sauran shirye-shiye kamar na, bunkasa sana’oi (MSMEDF), wanda zai mayar da hankali wajen tallafa wa sana’oin matasa (YEDP); da habaka shirin zuba jari don yin noma samun riba (AGSMEIS); da shirin samar da kudade ga masana’antu (CIFI); da shirin samar da rance na (CIFI); a cikin shirin Gidauniyar zuba jari na don a karfafa zuba jari na matasa (NYIF).

A karkashin shirin na (NYIF), CBN ya zuba Naira biliyan 75, inda manufar ita ce don a samar da ayyukan yi a tsakanin matasa domin rage radadin talauci da samar da ayyukan da za su kara bunkasa tattalin arzikin Nijeriya.

Bugu da kari, a cikin shirin na (NYIF), kudaden za CBN ya aminta a zuba sun kai daga Naira 250, 000 zuwa Naira miliyan 50, 000,000 CBN zai awaitar da hakan ne a tsawon shekaru uku wanda kuma babu kudin ruwa, inda duk CBN ya yi wannan ne, don kar matasa su zama masu dogaro da kansu, ba tare da jiran aikin gwamnati ba.

A zangon farko na 2022, wadanda suka amfana a fadin kasar nan sun kai 447,671, inda aka samar kasuwancin da yawansa ya kai 58,229, da kuma sauran kasuwancin da suka kai 389,442 da annobar Korona ta shafa.

Har ila yau, a bangaren MSMEDF da CBN ya samar da kudade ga ayyuka 488 a shirin MSME da ake gudanar wa daukacin fadin kasar nan inda wadannan ayyukan suka karade ayyuka guda 12 da ake yi a jihohi da kuma a fannin masana’antu masu zaman kansu dake, da fannin aikin noma, fannin kere-kere, fannin aikin noma, samar da makamashin hasken wutar lantarki da kuma hada – Gadar kasuwanci guda 216,706 tare da samar da ayyukan yi na kai tsaye da kuma wadanda ba na kai tsaye ba a daukacin fadin kasar nan.

Hakazalika, akwai kuma ayyukan na kasauwanci 55,422 wanda aka gudanar wa a karkashin shirin bunkasa Cibiyoyin kasuwanci (EDC) wanda shi ma an samar da dauki.

Wasu alkaluman sun nuna cewa, baya ga fannin aikin noma don samun riba 28,961 da kuma sauran ayyuka da CBN ya zuba kudade a cikin su yake kuma gudanar wa a daukacin fadin kasar nan, CBN ya kuma samar da ayyukan yi na kai tsaye da kuma wadanda ba na kai tsaye ba guda 107,932.

CBN ya yi wannan ne, karkashin shirin kanana da matsakaitan sana’oi na zuba jari wato (AgSMEIS), sannan CBN ya zuba kudade a cikin ayyukan horar da matasa sana’oin guda 395.

Sana’oin da za su amfana su ne, aikin noma, masana’antu, samar da makamashin wutar lantarki, kimiyya da sauransu.

Biyo bayan raguwar da aka samu na samar wa da Gwamnatin Tarayya da kudaden shiga, Babban Bankin Nijeriya CBN ya samar da kudade a cikin tsare-tsare da ke da bukatar a zuba kudaden ba kuma tare da, an ci karo da wata tangarda ba.

Gilbert sanannen mai fashin baki ne a fannin tattalin arziki kuma mazauni a Babbn Birnin Tarayyar Abuja.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Goron Jumu’a

Next Post

Neymar Ya Kafa Tarihi A PSG

Related

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025
Labaran Kasuwanci

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

3 weeks ago
Kuratan Sojoji 1,196 Aka Yaye A Makarantar Horar Da Sojoji Ta Zariya
Labaran Kasuwanci

Kuratan Sojoji 1,196 Aka Yaye A Makarantar Horar Da Sojoji Ta Zariya

1 month ago
Za Mu Tabbatar Da Samun Kyakkyawar Alaka Da Gwamnati Don Ci Gaban Kasuwar Kofar Ruwa – ‘Yanleman
Labaran Kasuwanci

Za Mu Tabbatar Da Samun Kyakkyawar Alaka Da Gwamnati Don Ci Gaban Kasuwar Kofar Ruwa – ‘Yanleman

7 months ago
Alternative Bank Shi Ne Mafi Inganci Da Baya Amfani Da KuÉ—in Ruwa Da Zuwa Da Fasaha A 2024
Labarai

Alternative Bank Shi Ne Mafi Inganci Da Baya Amfani Da KuÉ—in Ruwa Da Zuwa Da Fasaha A 2024

8 months ago
Kamfanin NNPCL Zai Cefanar Da Matatun Mai Na Kaduna Da Warri
Labarai

Kamfanin NNPCL Zai Cefanar Da Matatun Mai Na Kaduna Da Warri

11 months ago
Ministan Ma’adanai Ya Bukaci Masu Harkar Ma’adanai A Jihar Nasarawa Su Zauna Lafiya
Labaran Kasuwanci

Ministan Ma’adanai Ya Bukaci Masu Harkar Ma’adanai A Jihar Nasarawa Su Zauna Lafiya

11 months ago
Next Post
Neymar Ya Kafa Tarihi A PSG

Neymar Ya Kafa Tarihi A PSG

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Tsawaita Wa’adin Shugaban Kwastan Da Shekara ÆŠaya

Tinubu Ya Tsawaita Wa’adin Shugaban Kwastan Da Shekara ÆŠaya

July 31, 2025
Kare Ya Ciji Tsohon ÆŠan Wasan Barcelona A Mazakuta

Kare Ya Ciji Tsohon ÆŠan Wasan Barcelona A Mazakuta

July 31, 2025
An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina

An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina

July 31, 2025
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

2027: Ba Mu Kafa HaÉ—akarmu Don Cika Burin Atiku Ba – ADC

July 31, 2025
Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Ziyarci Jama’a, Ya Daina Sauraron Gwamnoni — ADC

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Ziyarci Jama’a, Ya Daina Sauraron Gwamnoni — ADC

July 31, 2025
Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza

Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza

July 31, 2025
Za A Kammala Aikin Titin Jirgin Ƙasan Kaduna-Kano A 2026 – Gwamnatin Tarayya

Za A Kammala Aikin Titin Jirgin Ƙasan Kaduna-Kano A 2026 – Gwamnatin Tarayya

July 31, 2025
Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

July 30, 2025
Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

July 30, 2025
Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

July 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.