ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tagomashin Da CBN Ya Samar Wajen Bunkasa Kanana Da Matsakaitan Sana’o’i

by Abubakar Abba
4 years ago
Noma

Bisa ga mayar da hankalin da Gwamnan Babban Bankin Nijeriya CBN Godwin Emefele ya yi a karkashin shugabancin bankin, ta hanyar kirkiro da tsare-tsare, musamman don ya karfafa wa masu kanana da matsakaitan sana’o’i (SMEs) a daukacin fadin kasar nan, ganin cewa fannin na (SMEs) na bayar da gagarumar gudunmawa wajen taimakawa da kara bunkasa tattalin arziki, bankin ya kirkiro da tsarin zuba kudade ga fannin kanana da matsakaitan sana’o’i.

Har ila yau, CBN a bisa duba na musamman a fannonin bayanai da sadarwa ta kimiyya (ICT), CBN ya kara bunkasa fannin don ya tafi kafada da kafa da na fadin duniya, musamman don a kara karfafa yin kere-kere da kara wa matasa kwarin gwiwar rungumar koyon sana’o’i.

  • Nasarar Tsarin CBN Na Samar Da Kudaden Habaka Tattalin Arzikin Nijeriya

Ganin cewa, Babban Bankin Nijeriya CBN na tafiya ne da zamani ya kuma yi amfani da fasahar zamani da ya kirkiro domin ganin ya habaka fannin na kanana da matsakaitan sana’oi SMEs.

ADVERTISEMENT

Hatta a daukacin fadin duniya, kasashen da suka ci gaba irin wannan tsarin ne suka runguma domin su kara bunkasa tattalin arzikinsu.

CBN a karkashin wannan shirin samar da daukin kudade a fannin na kanana da matsakaitan sana’oi, ya yi namiji kokarin wajen samar da daukin kudade ga SMEs, musamman domin a kara bunkasa fannin don a kara habaka tattalin arzikin Nijeriya, musamman fannin aikin noma da kere-kere.

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Ta Yi Asarar Biliyoyin Naira Saboda Dakatar Da Shigo Da Motoci Ta Iyakokinta

Farashin Siminti Zai Ragu Idan Farashin Kayan Aiki Ya Sauka – BUA

Alal misali, a bangaren fannin aikin noma, Emefele ya mayar da hankali a kanan da matsakaitan sana’oi ta hanyar shirin aikin noma na na ba da rance ‘Anchor Borrowers’ inda wannna shirin ya kutsa cikin daukacin fannonin aikin noma na kasar nan.

Har ila yau CBN ya samar da damarmaki ga wadanda za su amfana, CBN ya zuba a kai dauki kai tsaye don a karfafa kanana da matsakaitan sana’oi a cikin sauran shirye-shiye kamar na, bunkasa sana’oi (MSMEDF), wanda zai mayar da hankali wajen tallafa wa sana’oin matasa (YEDP); da habaka shirin zuba jari don yin noma samun riba (AGSMEIS); da shirin samar da kudade ga masana’antu (CIFI); da shirin samar da rance na (CIFI); a cikin shirin Gidauniyar zuba jari na don a karfafa zuba jari na matasa (NYIF).

A karkashin shirin na (NYIF), CBN ya zuba Naira biliyan 75, inda manufar ita ce don a samar da ayyukan yi a tsakanin matasa domin rage radadin talauci da samar da ayyukan da za su kara bunkasa tattalin arzikin Nijeriya.

Bugu da kari, a cikin shirin na (NYIF), kudaden za CBN ya aminta a zuba sun kai daga Naira 250, 000 zuwa Naira miliyan 50, 000,000 CBN zai awaitar da hakan ne a tsawon shekaru uku wanda kuma babu kudin ruwa, inda duk CBN ya yi wannan ne, don kar matasa su zama masu dogaro da kansu, ba tare da jiran aikin gwamnati ba.

A zangon farko na 2022, wadanda suka amfana a fadin kasar nan sun kai 447,671, inda aka samar kasuwancin da yawansa ya kai 58,229, da kuma sauran kasuwancin da suka kai 389,442 da annobar Korona ta shafa.

Har ila yau, a bangaren MSMEDF da CBN ya samar da kudade ga ayyuka 488 a shirin MSME da ake gudanar wa daukacin fadin kasar nan inda wadannan ayyukan suka karade ayyuka guda 12 da ake yi a jihohi da kuma a fannin masana’antu masu zaman kansu dake, da fannin aikin noma, fannin kere-kere, fannin aikin noma, samar da makamashin hasken wutar lantarki da kuma hada – Gadar kasuwanci guda 216,706 tare da samar da ayyukan yi na kai tsaye da kuma wadanda ba na kai tsaye ba a daukacin fadin kasar nan.

Hakazalika, akwai kuma ayyukan na kasauwanci 55,422 wanda aka gudanar wa a karkashin shirin bunkasa Cibiyoyin kasuwanci (EDC) wanda shi ma an samar da dauki.

Wasu alkaluman sun nuna cewa, baya ga fannin aikin noma don samun riba 28,961 da kuma sauran ayyuka da CBN ya zuba kudade a cikin su yake kuma gudanar wa a daukacin fadin kasar nan, CBN ya kuma samar da ayyukan yi na kai tsaye da kuma wadanda ba na kai tsaye ba guda 107,932.

CBN ya yi wannan ne, karkashin shirin kanana da matsakaitan sana’oi na zuba jari wato (AgSMEIS), sannan CBN ya zuba kudade a cikin ayyukan horar da matasa sana’oin guda 395.

Sana’oin da za su amfana su ne, aikin noma, masana’antu, samar da makamashin wutar lantarki, kimiyya da sauransu.

Biyo bayan raguwar da aka samu na samar wa da Gwamnatin Tarayya da kudaden shiga, Babban Bankin Nijeriya CBN ya samar da kudade a cikin tsare-tsare da ke da bukatar a zuba kudaden ba kuma tare da, an ci karo da wata tangarda ba.

Gilbert sanannen mai fashin baki ne a fannin tattalin arziki kuma mazauni a Babbn Birnin Tarayyar Abuja.

CBN
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Nijeriya Ta Yi Asarar Biliyoyin Naira Saboda Dakatar Da Shigo Da Motoci Ta Iyakokinta
Labaran Kasuwanci

Nijeriya Ta Yi Asarar Biliyoyin Naira Saboda Dakatar Da Shigo Da Motoci Ta Iyakokinta

May 29, 2026
Farashin Siminti Zai Ragu Idan Farashin Kayan Aiki Ya Sauka – BUA
Labaran Kasuwanci

Farashin Siminti Zai Ragu Idan Farashin Kayan Aiki Ya Sauka – BUA

May 21, 2026
Indomie Ta Sake Karrama Kwastominta A Gasar “Garabasar Samun Nasara” A Jihohin Arewacin Nijeriya
Labaran Kasuwanci

Indomie Ta Sake Karrama Kwastominta A Gasar “Garabasar Samun Nasara” A Jihohin Arewacin Nijeriya

April 21, 2026
Next Post
Neymar Ya Kafa Tarihi A PSG

Neymar Ya Kafa Tarihi A PSG

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.