• English
  • Business News
Friday, May 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taiwan Wani Yanki Ne Na Kasar Sin

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Taiwan Wani Yanki Ne Na Kasar Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanakin baya ne, sakataren harkokin wajen Amurka Anthony Blinken ya yi wasu kalamai da suka shafi yankin Taiwan na kasar Sin, kamar yadda ya saba. Idan ba a manta ba, a baya ma ya taba bayyanawa a yayin wata hira da aka yi da shi cewa,wai kasarsa na da kudurin tabbatar da cewa, yankin Taiwan zai iya kare kansa. Sai dai kuma Anthony Blinken, idan bai manta ba, ya bayyana a wani taron manyan jami’an kasashen Sin da Amurka da aka gudanar a karshen watan Oktoban shekarar da ta gabata, cewa Amurka za ta ci gaba da martaba manufar Sin daya tak a duniya”. Don haka, ta yaya mutumin da ke furta irin wadannan kalamai na kwan-gaba-kwan baya, ya dace da zama babban jami’in diflomasiyyar Amurka?

Ya kamata Blinken da sauran jami’an Amurka su fahimci cewa, yanzu haka akwai kasashe 180 a duniya, wadanda suka amince tare da goyon bayan manufar kasar Sin daya tak a duniya, kuma wannan ita ce yarjejeniya ta gaskiya da kasashen duniya suka amince da ita. Batun Taiwan, batu ne da ya shafi harkokin cikin gidan kasar Sin, kana babbar moriyar kasar mai muhimmanci, haka kuma shi ne tushen siyasa na alakar Sin da Amurka, kana jan layi na farko tsakaninsu wanda bai kamata a tsallaka shi ba.

Bugu da kari, dokar nan ta dangantakar Taiwan da Amurka da Amurkar ta kirkita, ta saba alkawurran da Amurkar ta dauka a cikin sanarwoyin hadin gwiwa guda uku da Sin da Amurka suka cimma a tsakaninsu. Idan maye ya manta, to uwar diya ba ta manta ba. A kokarin da kasar Sin ke yi na kara fahimtar da Amurka da ma kasashen duniya game da manufar kasar Sin daya tak a duniya, sanarwar da aka fitar bayan kammala cikakken zaman karo na shida na kwamitin tsakiya na JKS karo na 19, a kwanakin nan, ta bayyana karara cewa, kasar Sin za ta ci gaba da martaba ka’idar kasancewar Sin daya tak a duniya, da kuma matsaya irin wannan da aka cimma a shekarar 1992, wadda ke adawa da ayyukan ’yan aware dake neman ’yancin kai na Taiwan, da tsoma baki daga waje. Wannan ya nuna a fili irin tsayin daka na kasar Sin, da kuma matsayinta na kare ikon mallakar kasa, da cikakkun yankunanta da tsaro da moriyar ci gabanta. Koda a yayin zantawarsa da takwaransa na kasar Amurka Joe Biden ta kafar bidiyo a ranar Talata 16 ga watan Nuwanban shekarar 2022, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayyana matsayinsa bisa ka’ida game da batun Taiwan, inda ya jaddada aniyarsa ta yin kokarin sake hadewa da yankin cikin lumana bisa gaskiya da himma, amma idan ’yan aware masu neman ‘yancin kan Taiwan suka tunzura jama’a, ko suka zarce layin da aka shata, tilas ne a dauki tsauraran matakai.

Sanin kowa ne cewa, babban yankin kasar Sin, ya amince da jagoranci da himma a dangantakar dake tsakaninsa da zirin Taiwan, kuma batun sake hadewar kasar Sin, wani yanayi ne na tarihi da ba za a iya jurewa ba.

Don haka, kasar Sin tana jan kunnen bangaren Amurka da kada ya raina kudiri da karfin da jama’ar kasar Sin suke da shi, na kare ikon mallakar kasa da cikakkun yankanansu. Kuma duk wani mataki na kalubalantar manufar kasar Sin daya tak a duniya, da kokarin dakile kokarin sake dinkuwar kasar Sin baki daya, tabbas ba zai taba yin nasara ba. Don haka Amurka ta daina tsoma baki a harkokin cikin gidan Sin.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yansanda Sun Hana Jam’iyyu Siyasa Zagayen Murnar Nasarar Cin Zabe A Jihar Kebbi

Next Post

‘Yansanda Sun Cafke Ali Madakin Gini, Kan Zargin Amfani Da Bindiga A Yakin Zaben NNPP Na Kano

Related

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

5 hours ago
Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

7 hours ago
Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci
Daga Birnin Sin

Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

7 hours ago
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

8 hours ago
An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

9 hours ago
Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako
Daga Birnin Sin

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

11 hours ago
Next Post
‘Yansanda Sun Cafke Ali Madakin Gini, Kan Zargin Amfani Da Bindiga A Yakin Zaben NNPP Na Kano

'Yansanda Sun Cafke Ali Madakin Gini, Kan Zargin Amfani Da Bindiga A Yakin Zaben NNPP Na Kano

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

May 15, 2025
Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

May 15, 2025
Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

May 15, 2025
Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

May 15, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Samu Mummunan Sakamakon Jarabawar UTME 2025

May 15, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

May 15, 2025
An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

May 15, 2025
HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

May 15, 2025
Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

May 15, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.