• English
  • Business News
Saturday, September 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taiwan Wani Yanki Ne Na Kasar Sin

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Taiwan Wani Yanki Ne Na Kasar Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanakin baya ne, sakataren harkokin wajen Amurka Anthony Blinken ya yi wasu kalamai da suka shafi yankin Taiwan na kasar Sin, kamar yadda ya saba. Idan ba a manta ba, a baya ma ya taba bayyanawa a yayin wata hira da aka yi da shi cewa,wai kasarsa na da kudurin tabbatar da cewa, yankin Taiwan zai iya kare kansa. Sai dai kuma Anthony Blinken, idan bai manta ba, ya bayyana a wani taron manyan jami’an kasashen Sin da Amurka da aka gudanar a karshen watan Oktoban shekarar da ta gabata, cewa Amurka za ta ci gaba da martaba manufar Sin daya tak a duniya”. Don haka, ta yaya mutumin da ke furta irin wadannan kalamai na kwan-gaba-kwan baya, ya dace da zama babban jami’in diflomasiyyar Amurka?

Ya kamata Blinken da sauran jami’an Amurka su fahimci cewa, yanzu haka akwai kasashe 180 a duniya, wadanda suka amince tare da goyon bayan manufar kasar Sin daya tak a duniya, kuma wannan ita ce yarjejeniya ta gaskiya da kasashen duniya suka amince da ita. Batun Taiwan, batu ne da ya shafi harkokin cikin gidan kasar Sin, kana babbar moriyar kasar mai muhimmanci, haka kuma shi ne tushen siyasa na alakar Sin da Amurka, kana jan layi na farko tsakaninsu wanda bai kamata a tsallaka shi ba.

Bugu da kari, dokar nan ta dangantakar Taiwan da Amurka da Amurkar ta kirkita, ta saba alkawurran da Amurkar ta dauka a cikin sanarwoyin hadin gwiwa guda uku da Sin da Amurka suka cimma a tsakaninsu. Idan maye ya manta, to uwar diya ba ta manta ba. A kokarin da kasar Sin ke yi na kara fahimtar da Amurka da ma kasashen duniya game da manufar kasar Sin daya tak a duniya, sanarwar da aka fitar bayan kammala cikakken zaman karo na shida na kwamitin tsakiya na JKS karo na 19, a kwanakin nan, ta bayyana karara cewa, kasar Sin za ta ci gaba da martaba ka’idar kasancewar Sin daya tak a duniya, da kuma matsaya irin wannan da aka cimma a shekarar 1992, wadda ke adawa da ayyukan ’yan aware dake neman ’yancin kai na Taiwan, da tsoma baki daga waje. Wannan ya nuna a fili irin tsayin daka na kasar Sin, da kuma matsayinta na kare ikon mallakar kasa, da cikakkun yankunanta da tsaro da moriyar ci gabanta. Koda a yayin zantawarsa da takwaransa na kasar Amurka Joe Biden ta kafar bidiyo a ranar Talata 16 ga watan Nuwanban shekarar 2022, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayyana matsayinsa bisa ka’ida game da batun Taiwan, inda ya jaddada aniyarsa ta yin kokarin sake hadewa da yankin cikin lumana bisa gaskiya da himma, amma idan ’yan aware masu neman ‘yancin kan Taiwan suka tunzura jama’a, ko suka zarce layin da aka shata, tilas ne a dauki tsauraran matakai.

Sanin kowa ne cewa, babban yankin kasar Sin, ya amince da jagoranci da himma a dangantakar dake tsakaninsa da zirin Taiwan, kuma batun sake hadewar kasar Sin, wani yanayi ne na tarihi da ba za a iya jurewa ba.

Don haka, kasar Sin tana jan kunnen bangaren Amurka da kada ya raina kudiri da karfin da jama’ar kasar Sin suke da shi, na kare ikon mallakar kasa da cikakkun yankanansu. Kuma duk wani mataki na kalubalantar manufar kasar Sin daya tak a duniya, da kokarin dakile kokarin sake dinkuwar kasar Sin baki daya, tabbas ba zai taba yin nasara ba. Don haka Amurka ta daina tsoma baki a harkokin cikin gidan Sin.

Labarai Masu Nasaba

Sin Da Amurka Na Iya Cimma Manyan Nasara Tare In Ji Shugaba Xi

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yansanda Sun Hana Jam’iyyu Siyasa Zagayen Murnar Nasarar Cin Zabe A Jihar Kebbi

Next Post

‘Yansanda Sun Cafke Ali Madakin Gini, Kan Zargin Amfani Da Bindiga A Yakin Zaben NNPP Na Kano

Related

Sin Da Amurka Na Iya Cimma Manyan Nasara Tare In Ji Shugaba Xi
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Na Iya Cimma Manyan Nasara Tare In Ji Shugaba Xi

15 minutes ago
Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu
Daga Birnin Sin

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

18 hours ago
An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan
Daga Birnin Sin

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

19 hours ago
Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

20 hours ago
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

21 hours ago
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata
Daga Birnin Sin

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

22 hours ago
Next Post
‘Yansanda Sun Cafke Ali Madakin Gini, Kan Zargin Amfani Da Bindiga A Yakin Zaben NNPP Na Kano

'Yansanda Sun Cafke Ali Madakin Gini, Kan Zargin Amfani Da Bindiga A Yakin Zaben NNPP Na Kano

LABARAI MASU NASABA

Mun Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai Na Shekara 50 A Nijeriya – Matatar Dangote

Mun Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai Na Shekara 50 A Nijeriya – Matatar Dangote

September 20, 2025
Sin Da Amurka Na Iya Cimma Manyan Nasara Tare In Ji Shugaba Xi

Sin Da Amurka Na Iya Cimma Manyan Nasara Tare In Ji Shugaba Xi

September 20, 2025
Ta Yaya Zan Yi Tattalin Mijina?

Ta Yaya Zan Yi Tattalin Mijina?

September 20, 2025
Ajali: Wasu Ƴan Ƙauye Sun Gujewa Ƴan Bindiga Sun Nutse A Ruwa

Ajali: Wasu Ƴan Ƙauye Sun Gujewa Ƴan Bindiga Sun Nutse A Ruwa

September 20, 2025
Tinubu Ya Halarci Ɗaurin Auren Ɗan Yari, Ya Kai Ziyara Gidan Tsohon Shugaban Ƙasa Buhari

Tinubu Ya Halarci Ɗaurin Auren Ɗan Yari, Ya Kai Ziyara Gidan Tsohon Shugaban Ƙasa Buhari

September 20, 2025
Sabon Kakin Ƴansanda Ya Ziyarci Cibiyar Ƙungiyar Ƴan Jarida A FCT

Sabon Kakin Ƴansanda Ya Ziyarci Cibiyar Ƙungiyar Ƴan Jarida A FCT

September 20, 2025
Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi

Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi

September 20, 2025
Makarantun Da Ba Ƙwararrun Malamai Za Su Rasa Zama Cibiyar Rubuta Jarrabawar NECO

Makarantun Da Ba Ƙwararrun Malamai Za Su Rasa Zama Cibiyar Rubuta Jarrabawar NECO

September 20, 2025
Magoya Bayan Aiyedatiwa Sun Ɓarke Da Sowa Bayan Nasara A Kotun Ƙoli

Magoya Bayan Aiyedatiwa Sun Ɓarke Da Sowa Bayan Nasara A Kotun Ƙoli

September 20, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunƙurin Kawar Da Shanu Daga Titunan Abuja

Gwamnatin Tarayya Na Yunƙurin Kawar Da Shanu Daga Titunan Abuja

September 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.