• English
  • Business News
Monday, September 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Takaicin Fyaden Kananan Yara Ya Sa Na Shirya Fim Din AKASI – Yakubu Gwammaja

by Rabi'at Sidi Bala
1 year ago
in Nishadi
0
Takaicin Fyaden Kananan Yara Ya Sa Na Shirya Fim Din AKASI – Yakubu Gwammaja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shirin fim din AKASI shiri ne mai dogon zango, wanda aka fara sakin sa ranar 7 ga Maris, 2024. Da yake an jima ana dakon lokacin sakinsa,  Rumbun Nishadi ya ji ta bakin mashiryin fim din YAKUBU PRODUCER GWAMMAJA game da abin da ya kunsa da kuma sauran batutuwa kamar yadda za ku ji a tattaunawarsa da wakiliyarmu, RABI’AT SIDI BALA kamar haka:

abatarwa, ya cikakken sunanka?

Sunana Yakubu Bala wanda aka fi sani da Yakubu Gwammaja.

Me ya ja hankalinka har ka shirya shirin AKASI, kuma a kan me yake magana?

Yawan fyade da ake yi wa kananan yara abin yana min ciwo matuka, da kuma take gaskiya wajan masu wadata.

Labarai Masu Nasaba

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba

Shin labarin AKASI gaskiya ne ko kuma kirkirarren labari ne?

Gaskiya labarin Akasi kirkira ne, amma yana faruwa a gaske tunda ai yanzu zalinci ya zama ruwan dare mai kudi ya take talaka duk ba wani sabon abu bane a wannan doron duniya.

Ya batun kudaden da aka kashe wajen gudanar da shirin, kana ganin kwalliya za ta biya kudin sabulu wajen mayar da kudadden da aka kashe ko kuwa?

Gaskiya an kashe kudi har sai da ta-kai-ta-kawo ina jin haushin kashe su tabbas a aljihuna suke fita har ta sa na kasa jituwa da duk wanda zai damu ‘ed producer’ a kan tambayar a karo kudi duba da yadda na ga yana kokari matuka tun daga abinci biyan kowa hakkinsa da mu kanmu manyan ma’aikata babu wanda Baba Hayatu ya tauyewa hakki ma sha Allah. Kuma karshe kwalliya ta biya kudin sabulu manyan gidajen suka rika nemansa domin ganin sun saya sun saka gidajen tb nasu, a karshe aka daidaita da DStb suke haskawa, a YouTube kuma muryar Hausa tb duk Alhamis misalin karfe takwas da rabi na dare.

Ya batun tattara jarumai dan gudanar da shirin, shin ka samu wani kalubale daga wannan bangaren ko wani banfaren daban game da shirun AKASI ko kuwa babu wani kalubale?

A gaskiya tunda nake shirin fim sama da shekara ashirin ban taba fim mai wuyar Akasi ba, idan ka cire wani fim dina mutanen farko, Akasi ya hada jarumai masu yawan gaske jiya da yau, idan ka ce za kai aiki da wanda ya manta aiki tsawan shekara goma baya gwagwarmaya tabbas ba karamin kalubale bane, domin a lokacinsu idan jarumi ya zo ya kan fadi lokacin zuwansa da tafiya, sabanin yanzu ‘series film’ idan ka zo ‘day one’ kawai ka zo ne sai an tashi ka tafi, amma wata wanda na sakaya sunanta babbar jaruma ce ada ta kan ce awa daya na baku idan baku gama ba wallahi tafiya zan yi, aikuwa cikin ikon Allah ba ta karawa mun sami kalubale iri daban-daban, saboda yawan mutanan da aka tara da yawan gidan labarin yayi yawa, har sai da na ce mai ya sa muka sa gidaje haka da yawa.

Ya ka ke kallon karbuwar shirin wajen masu kallo musamman yadda yake sauka a yanzu?

Shirin Akasi ban so ya zo a lokacin Ramadan ba kowa ya san fim idan bai amsa kira ba ya zo a lokacin azumi bai fiya samin magoya baya ba, amma duk da haka Alhamdulilah ana kallo gaskiya, amma na san bayan azumi kowa zai koma daga baya ya gani ya ga mene ne ya faru musamman yadda ya fara daukar dumi yanzu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Batutuwan Diflomasiyya Da Aka Amincewa Yayin Taron Beijing Sun Haskaka Ma’anar Dimokaradiyya

Next Post

Ya Kamata Amurka Ta Yiwa Duniya Bayani Game Da Matsalolin Da Jiragen Kamfanin Boeing Ke Fuskanta

Related

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)
Nishadi

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

1 day ago
Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba
Nishadi

Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba

1 week ago
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah
Nishadi

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

2 weeks ago
Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya
Nishadi

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya

3 weeks ago
Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu
Nishadi

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

4 weeks ago
Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya
Nishadi

Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

4 weeks ago
Next Post
Ya Kamata Amurka Ta Yiwa Duniya Bayani Game Da Matsalolin Da Jiragen Kamfanin Boeing Ke Fuskanta

Ya Kamata Amurka Ta Yiwa Duniya Bayani Game Da Matsalolin Da Jiragen Kamfanin Boeing Ke Fuskanta

LABARAI MASU NASABA

AKASI

Jarin Da Sin Ta Zuba Kai Tsaye A Kasashe Cikin Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ya Karu Da Kashi 22.9% A 2024

September 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

September 8, 2025
Adadin Kamfanonin AI A Sin Sun Haura 5,000

Adadin Kamfanonin AI A Sin Sun Haura 5,000

September 8, 2025
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Buƙaci Al’ummar Jihar Kaduna Da Su Yi Rijistar Katin Zaɓe 

September 8, 2025
Xi Ya Halarci Taron Kungiyar BRICS Ta Yanar Gizo

Xi Ya Halarci Taron Kungiyar BRICS Ta Yanar Gizo

September 8, 2025
DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu

DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu

September 8, 2025
PDP Ta Zama Fanko, Ta Rasa Komai– Dele Momodu

PDP Ta Zama Fanko, Ta Rasa Komai– Dele Momodu

September 8, 2025
Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

September 8, 2025
Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

September 8, 2025
Sanata Natasha Zata Dawo Aiki Bayan Dakatarwar Wata Shida

Sanata Natasha Zata Dawo Aiki Bayan Dakatarwar Wata Shida

September 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.