• English
  • Business News
Wednesday, June 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Takaicin Fyaden Kananan Yara Ya Sa Na Shirya Fim Din AKASI – Yakubu Gwammaja

by Rabi'at Sidi Bala
1 year ago
in Nishadi
0
Takaicin Fyaden Kananan Yara Ya Sa Na Shirya Fim Din AKASI – Yakubu Gwammaja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shirin fim din AKASI shiri ne mai dogon zango, wanda aka fara sakin sa ranar 7 ga Maris, 2024. Da yake an jima ana dakon lokacin sakinsa,  Rumbun Nishadi ya ji ta bakin mashiryin fim din YAKUBU PRODUCER GWAMMAJA game da abin da ya kunsa da kuma sauran batutuwa kamar yadda za ku ji a tattaunawarsa da wakiliyarmu, RABI’AT SIDI BALA kamar haka:

abatarwa, ya cikakken sunanka?

Sunana Yakubu Bala wanda aka fi sani da Yakubu Gwammaja.

Me ya ja hankalinka har ka shirya shirin AKASI, kuma a kan me yake magana?

Yawan fyade da ake yi wa kananan yara abin yana min ciwo matuka, da kuma take gaskiya wajan masu wadata.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

Shin labarin AKASI gaskiya ne ko kuma kirkirarren labari ne?

Gaskiya labarin Akasi kirkira ne, amma yana faruwa a gaske tunda ai yanzu zalinci ya zama ruwan dare mai kudi ya take talaka duk ba wani sabon abu bane a wannan doron duniya.

Ya batun kudaden da aka kashe wajen gudanar da shirin, kana ganin kwalliya za ta biya kudin sabulu wajen mayar da kudadden da aka kashe ko kuwa?

Gaskiya an kashe kudi har sai da ta-kai-ta-kawo ina jin haushin kashe su tabbas a aljihuna suke fita har ta sa na kasa jituwa da duk wanda zai damu ‘ed producer’ a kan tambayar a karo kudi duba da yadda na ga yana kokari matuka tun daga abinci biyan kowa hakkinsa da mu kanmu manyan ma’aikata babu wanda Baba Hayatu ya tauyewa hakki ma sha Allah. Kuma karshe kwalliya ta biya kudin sabulu manyan gidajen suka rika nemansa domin ganin sun saya sun saka gidajen tb nasu, a karshe aka daidaita da DStb suke haskawa, a YouTube kuma muryar Hausa tb duk Alhamis misalin karfe takwas da rabi na dare.

Ya batun tattara jarumai dan gudanar da shirin, shin ka samu wani kalubale daga wannan bangaren ko wani banfaren daban game da shirun AKASI ko kuwa babu wani kalubale?

A gaskiya tunda nake shirin fim sama da shekara ashirin ban taba fim mai wuyar Akasi ba, idan ka cire wani fim dina mutanen farko, Akasi ya hada jarumai masu yawan gaske jiya da yau, idan ka ce za kai aiki da wanda ya manta aiki tsawan shekara goma baya gwagwarmaya tabbas ba karamin kalubale bane, domin a lokacinsu idan jarumi ya zo ya kan fadi lokacin zuwansa da tafiya, sabanin yanzu ‘series film’ idan ka zo ‘day one’ kawai ka zo ne sai an tashi ka tafi, amma wata wanda na sakaya sunanta babbar jaruma ce ada ta kan ce awa daya na baku idan baku gama ba wallahi tafiya zan yi, aikuwa cikin ikon Allah ba ta karawa mun sami kalubale iri daban-daban, saboda yawan mutanan da aka tara da yawan gidan labarin yayi yawa, har sai da na ce mai ya sa muka sa gidaje haka da yawa.

Ya ka ke kallon karbuwar shirin wajen masu kallo musamman yadda yake sauka a yanzu?

Shirin Akasi ban so ya zo a lokacin Ramadan ba kowa ya san fim idan bai amsa kira ba ya zo a lokacin azumi bai fiya samin magoya baya ba, amma duk da haka Alhamdulilah ana kallo gaskiya, amma na san bayan azumi kowa zai koma daga baya ya gani ya ga mene ne ya faru musamman yadda ya fara daukar dumi yanzu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Batutuwan Diflomasiyya Da Aka Amincewa Yayin Taron Beijing Sun Haskaka Ma’anar Dimokaradiyya

Next Post

Ya Kamata Amurka Ta Yiwa Duniya Bayani Game Da Matsalolin Da Jiragen Kamfanin Boeing Ke Fuskanta

Related

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu
Nishadi

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

4 days ago
Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 
Nishadi

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

2 weeks ago
Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani
Nishadi

Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani

2 weeks ago
Ban Ɗauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa
Nishadi

Ban Ɗauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa

2 weeks ago
Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro
Nishadi

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

3 weeks ago
Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage
Nishadi

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

3 weeks ago
Next Post
Ya Kamata Amurka Ta Yiwa Duniya Bayani Game Da Matsalolin Da Jiragen Kamfanin Boeing Ke Fuskanta

Ya Kamata Amurka Ta Yiwa Duniya Bayani Game Da Matsalolin Da Jiragen Kamfanin Boeing Ke Fuskanta

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

June 4, 2025
Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

June 4, 2025
Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

June 4, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

June 4, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

June 4, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 

June 4, 2025
Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

June 4, 2025
DSS

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

June 4, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 4, 2025
katsina

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Hadin Gwiwa Da ‘Yan Kasuwa Domin Cigaban Jihar

June 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.