ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Takaicin Fyaden Kananan Yara Ya Sa Na Shirya Fim Din AKASI – Yakubu Gwammaja

by Rabi'at Sidi Bala
2 years ago
AKASI

Shirin fim din AKASI shiri ne mai dogon zango, wanda aka fara sakin sa ranar 7 ga Maris, 2024. Da yake an jima ana dakon lokacin sakinsa,  Rumbun Nishadi ya ji ta bakin mashiryin fim din YAKUBU PRODUCER GWAMMAJA game da abin da ya kunsa da kuma sauran batutuwa kamar yadda za ku ji a tattaunawarsa da wakiliyarmu, RABI’AT SIDI BALA kamar haka:

abatarwa, ya cikakken sunanka?

Sunana Yakubu Bala wanda aka fi sani da Yakubu Gwammaja.

ADVERTISEMENT

Me ya ja hankalinka har ka shirya shirin AKASI, kuma a kan me yake magana?

Yawan fyade da ake yi wa kananan yara abin yana min ciwo matuka, da kuma take gaskiya wajan masu wadata.

LABARAI MASU NASABA

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa

Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

Shin labarin AKASI gaskiya ne ko kuma kirkirarren labari ne?

Gaskiya labarin Akasi kirkira ne, amma yana faruwa a gaske tunda ai yanzu zalinci ya zama ruwan dare mai kudi ya take talaka duk ba wani sabon abu bane a wannan doron duniya.

Ya batun kudaden da aka kashe wajen gudanar da shirin, kana ganin kwalliya za ta biya kudin sabulu wajen mayar da kudadden da aka kashe ko kuwa?

Gaskiya an kashe kudi har sai da ta-kai-ta-kawo ina jin haushin kashe su tabbas a aljihuna suke fita har ta sa na kasa jituwa da duk wanda zai damu ‘ed producer’ a kan tambayar a karo kudi duba da yadda na ga yana kokari matuka tun daga abinci biyan kowa hakkinsa da mu kanmu manyan ma’aikata babu wanda Baba Hayatu ya tauyewa hakki ma sha Allah. Kuma karshe kwalliya ta biya kudin sabulu manyan gidajen suka rika nemansa domin ganin sun saya sun saka gidajen tb nasu, a karshe aka daidaita da DStb suke haskawa, a YouTube kuma muryar Hausa tb duk Alhamis misalin karfe takwas da rabi na dare.

Ya batun tattara jarumai dan gudanar da shirin, shin ka samu wani kalubale daga wannan bangaren ko wani banfaren daban game da shirun AKASI ko kuwa babu wani kalubale?

A gaskiya tunda nake shirin fim sama da shekara ashirin ban taba fim mai wuyar Akasi ba, idan ka cire wani fim dina mutanen farko, Akasi ya hada jarumai masu yawan gaske jiya da yau, idan ka ce za kai aiki da wanda ya manta aiki tsawan shekara goma baya gwagwarmaya tabbas ba karamin kalubale bane, domin a lokacinsu idan jarumi ya zo ya kan fadi lokacin zuwansa da tafiya, sabanin yanzu ‘series film’ idan ka zo ‘day one’ kawai ka zo ne sai an tashi ka tafi, amma wata wanda na sakaya sunanta babbar jaruma ce ada ta kan ce awa daya na baku idan baku gama ba wallahi tafiya zan yi, aikuwa cikin ikon Allah ba ta karawa mun sami kalubale iri daban-daban, saboda yawan mutanan da aka tara da yawan gidan labarin yayi yawa, har sai da na ce mai ya sa muka sa gidaje haka da yawa.

Ya ka ke kallon karbuwar shirin wajen masu kallo musamman yadda yake sauka a yanzu?

Shirin Akasi ban so ya zo a lokacin Ramadan ba kowa ya san fim idan bai amsa kira ba ya zo a lokacin azumi bai fiya samin magoya baya ba, amma duk da haka Alhamdulilah ana kallo gaskiya, amma na san bayan azumi kowa zai koma daga baya ya gani ya ga mene ne ya faru musamman yadda ya fara daukar dumi yanzu.

AKASI
Rabi'at Sidi Bala
+ postsBio
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Yadda Alaƙata Da Adamu Zango Ta Bunƙasa A Kannywood —Jarumi Ibrahim Sodangi 
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Fim Ko Gaske:Yaushe Masu Kallon Fina-finai Za Su Daina Daukar Fim A Matsayin Gaske
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Fim ɗin ƙaddara: Anya Ana Samun Irin Wannan ƙaddarar Kuwa?
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

MASU ALAKA

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
Nishadi

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa

September 5, 2026
Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood
Nishadi

Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

August 29, 2026
AKASI
Nishadi

Dalilan Da Suka Sa Ba Zan Iya Auren Ɗan Film Ba —Bilkisu Bishasha

August 23, 2026
Next Post
Ya Kamata Amurka Ta Yiwa Duniya Bayani Game Da Matsalolin Da Jiragen Kamfanin Boeing Ke Fuskanta

Ya Kamata Amurka Ta Yiwa Duniya Bayani Game Da Matsalolin Da Jiragen Kamfanin Boeing Ke Fuskanta

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.