• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Takarar Musulmi 2: Magoyan Bayan APC Sun Yi Zanga-zanga A Legas, Sun Bukaci A Sauya Shettima

by Abubakar Abba
3 years ago
APC

Daruruwan masu ruwa da tsaki a jam’iyyar APC a jihar Legas sun gudanar da zanga-zangar lumana a kan wasu titunan da ke a jihar, inda suka nuna bara’a a kan bin tsarin takarar Musulmai biyu da APC ta bullo da shi don tunkarar zaben shugaban kasa a 2023. 

Zanga-zangar wacce ta gudana a jiya Litinin, an yi ta ne a karkashin inuwar hadakar masu ruwa da tsaki na APC da kuma magoya bayan APC da suka fito daga Kudu maso Gabas.

  • Sin: Cinikin Kayayyakin Abinci Zai Kara Amfanawa Jama’ar Sin Da Afirka
  • Yawan Kayayyakin Masana’antu Na Kasar Sin Ya Karu Da Kaso 3.5 Cikin Watanni Bakwai Na Farko

Sun yi tattaki daga babban shagon Shoprite da ke a yankin Ikeja zuwa Majalisar Dokoki ta jihar da ke yankin Alausa, inda suke yin wake-waken tare da dauke da kwalayen da suka yi rubuce-rubucen cewa, Asiwaju ka sauya sunan Shettima a matsayin mataimakinka, ya kamata shugaba Buhari da Tinubu su sake yin tunani a kan tsarin takarar Musulmai biyu.

A jawabin da ya yi wa manema labarai a yayin zanga-zangar mai magana da yawun masu zanga-zangar, Samuel Arokoyo, ya sanar da cewa, matsalar da kawai APC za ta fuskanta a zaben 2023 shi ne yadda Tinubu ya dauko Shettima a matsayin mataimakinsa.

Arokoyo, ya nanata cewa amma inda Tinubu ya dauko dan Arewa kirista a matsayin mataimakinsa, zai iya samun kuri’un Kiritoci kashi 70 a cikin dari musamman daga jihohin Kogi, Kwara, Filato, Nasarawa, Benue, Taraba, Kaduna, Adamawa, Gombe, Borno, da Abuja

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

Wannan zanga-zangar dai ta biyo bayan makamanciyar wacce aka yi a yau wata daya sakakatariyar APC ta kasa da ke Abuja, inda masu zanga-zangar suka nuna bacin ransu kan tsarin na ‘yan takara Musulmai biyu.

Har ila yau, an kuma gudanar da makamanciyar irin wannan zanga-zangar a yayin da shugabanin APC na kasa suka kaddamar da Kashim Shettima a matsayin mataimakin Tinubu a dakin taro na Shehu Musa Yar’Adua da ke Abuja, inda masu zanga-zangar suka bukaci a sauya sunan Shettima da wani dan takara Kirista.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha
Siyasa

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump
Labarai

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
Manyan Labarai

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Next Post
Ku Tuhumi PDP Kan Yajin Aikin ASUU – Keyamo Ga ‘Yan Nijeriya

Ku Tuhumi PDP Kan Yajin Aikin ASUU - Keyamo Ga 'Yan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
tinubu

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

November 4, 2025
2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

November 4, 2025
Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

November 4, 2025
Karancin Abinci: Kofar Ofishin Tinubu A Rufe Take, Har Wasu Ministoci Ba Su Iya Ganinsa – Ndume 

Zargin Kisan Kiyashi Ga Kiristoci: Trump Bai San Ƙalubalen Tsaron Da Najeriya Ke Ciki Ba — Ndume

November 4, 2025
Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.