ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Takarar Musulmi 2: Magoyan Bayan APC Sun Yi Zanga-zanga A Legas, Sun Bukaci A Sauya Shettima

by Abubakar Abba
4 years ago
APC

Daruruwan masu ruwa da tsaki a jam’iyyar APC a jihar Legas sun gudanar da zanga-zangar lumana a kan wasu titunan da ke a jihar, inda suka nuna bara’a a kan bin tsarin takarar Musulmai biyu da APC ta bullo da shi don tunkarar zaben shugaban kasa a 2023. 

Zanga-zangar wacce ta gudana a jiya Litinin, an yi ta ne a karkashin inuwar hadakar masu ruwa da tsaki na APC da kuma magoya bayan APC da suka fito daga Kudu maso Gabas.

  • Sin: Cinikin Kayayyakin Abinci Zai Kara Amfanawa Jama’ar Sin Da Afirka
  • Yawan Kayayyakin Masana’antu Na Kasar Sin Ya Karu Da Kaso 3.5 Cikin Watanni Bakwai Na Farko

Sun yi tattaki daga babban shagon Shoprite da ke a yankin Ikeja zuwa Majalisar Dokoki ta jihar da ke yankin Alausa, inda suke yin wake-waken tare da dauke da kwalayen da suka yi rubuce-rubucen cewa, Asiwaju ka sauya sunan Shettima a matsayin mataimakinka, ya kamata shugaba Buhari da Tinubu su sake yin tunani a kan tsarin takarar Musulmai biyu.

ADVERTISEMENT

A jawabin da ya yi wa manema labarai a yayin zanga-zangar mai magana da yawun masu zanga-zangar, Samuel Arokoyo, ya sanar da cewa, matsalar da kawai APC za ta fuskanta a zaben 2023 shi ne yadda Tinubu ya dauko Shettima a matsayin mataimakinsa.

Arokoyo, ya nanata cewa amma inda Tinubu ya dauko dan Arewa kirista a matsayin mataimakinsa, zai iya samun kuri’un Kiritoci kashi 70 a cikin dari musamman daga jihohin Kogi, Kwara, Filato, Nasarawa, Benue, Taraba, Kaduna, Adamawa, Gombe, Borno, da Abuja

LABARAI MASU NASABA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna

Wannan zanga-zangar dai ta biyo bayan makamanciyar wacce aka yi a yau wata daya sakakatariyar APC ta kasa da ke Abuja, inda masu zanga-zangar suka nuna bacin ransu kan tsarin na ‘yan takara Musulmai biyu.

Har ila yau, an kuma gudanar da makamanciyar irin wannan zanga-zangar a yayin da shugabanin APC na kasa suka kaddamar da Kashim Shettima a matsayin mataimakin Tinubu a dakin taro na Shehu Musa Yar’Adua da ke Abuja, inda masu zanga-zangar suka bukaci a sauya sunan Shettima da wani dan takara Kirista.

APC
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna
Siyasa

Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna

September 9, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Next Post
Ku Tuhumi PDP Kan Yajin Aikin ASUU – Keyamo Ga ‘Yan Nijeriya

Ku Tuhumi PDP Kan Yajin Aikin ASUU - Keyamo Ga 'Yan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.