• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Takardun Kudin Da Suka Shaida Yadda Kasashen Duniya Suka Ci Gajiyar Ci Gaban Kasar Sin

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Takardun Kudin Da Suka Shaida Yadda Kasashen Duniya Suka Ci Gajiyar Ci Gaban Kasar Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jama’a, in kun yi la’akari da takardun kudi na kasa da kasa, za ku gano da cewa, hotunan da aka buga a takardun kudi na wasu kasashen Afirka, da ma sauran wasu kasashe masu tasowa, suna da alaka da kasar Sin.

Zanenmu na yau ya kuma nuna wasu abubuwan da aka buga a takardun kudi na kasashen Aljeriya, da Sudan, da Madagarscar da Malawi, wadanda suke da alaka da kasar Sin.

  • Tattalin Arzikin Kasar Sin Na Ci Gaba Da Farfadowa A Bana

In mun dauki takardun kudi na Aljeriya ga misali, za mu ga cewa, an buga hoton babban masallacin kasar da aka sanyawa sunan Djamaa el Djazaïr, a takardun kudin kasar mai darajar Dinar 1000, masallacin da ma’aikatan kasar Sin suka shafe tsawon shekaru shida suna ginawa, bayan daidaita wahalhalu da dama da suka fuskanta.

An kaddamar da masallacin ne a shekarar 2017, wanda ke iya daukar musulmi kimanin dubu 36 a lokaci guda, wanda kuma ya kasance babban masallaci mafi girma na farko a nahiyar Afirka, kuma na uku a duniya baki daya.

Sai kuma a takardun kudin kasar masu darajar Dinar 500, inda aka buga hoton tauraron dan Adam na sadarwa na farko a kansa, tauraron da ya kasance irinsa na farko a kasar, wanda kasar Sin ta yi nazarinsa tare da harba shi a shekarar 2017, wanda ya taimaka wajen daidaita matsalolin sadarwa da suka shafi rediyo, da talabijin da yanar gizo, da samar da ilmi da sauransu a kasar.

Labarai Masu Nasaba

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Baya ga haka, a kasar Sudan, madatsar ruwa ta Upper Atbara da kamfanin kasar Sin ya dauki nauyin ginawa, ta taka muhimmiyar rawa wajen daidaita matsalolin samar da wutar lantarki, da ruwan sha, da kuma ban ruwa ga miliyoyin al’ummar kasar, wadda kuma ta samar da gudummawar bunkasa tattalin arziki da zaman rayuwar al’umma na kasar.

Sai kuma a Madagarscar, fasahar inganta irin shinkafa da masanan ilmin noma na kasar Sin suka samar ta sa yawan shinkafar da aka samar a kasar ta karu da yawan gaske, matakin da ya daidaita matsalar abinci ga al’ummar kasar da ke yawan dogara ga shinkafa. Domin bayyana godiyarsu, kasashen biyu sun buga hotunansu a takardun kudin su.

Hakika, irin wadannan labarai ba sa lisaftuwa. Cikin shekaru 10 da suka wuce, bisa ga shawarar Ziri Daya da Hanya Daya, an aiwatar da shirye-shiryen gina gadoji, da tashoshin jiragen ruwa, da hanyoyin mota, da layukan dogo, da tashoshin samar da wuta, da filayen wasa da dai sauransu da dama a kasashen Afirka da ma sauran kasashe masu tasowa, wadanda suka ba da babbar gudummawa ga bunkasuwar kasashen, da ma rayuwar al’ummominsu.

A yayin da kasar Sin ta samu gaggarumin ci gaban tattalin arziki da zaman al’umma, ta kuma yi kokarin raba nasarorinta ga sauran kasashen duniya, kasancewarta tana rungumar makomar dan Adam ta bai daya.

Kwanan nan, an bude babban taron wakilan jam’iyyar kwaminis da ke kan karagar mulki a kasar Sin ko (JKS) karo na 20, kuma a rahoton da ya gabatar wajen taron, babban sakataren kwamitin kolin jam’iyyar mista Xi Jinping ya yi nuni da cewa, kasar Sin za ta karfafa hadin gwiwa da kasashe masu tasowa bisa sahihanci da gaskiya, don kiyaye moriyarsu ta bai daya. A sa’i daya, kasar ta kuma, yi kira ga kasashen duniya da su yayata manufar kishin zaman lafiya, da ci gaba, da adalci, da dimokuradiyya da ‘yanci, don al’ummomin kasashe daban daban su kara kishin juna, su kuma martaba mabambantan wayewar kan duniya, su kara yin mu’amala da juna ta fannin al’adu, ta yadda za su kawar da sabani da rikice-rikice da suke fuskanta.

Zaman duniya, cude-ni-in-cude-ka ne. A ganin kasar Sin, da ci gaban duniya baki daya za a tabbatar da ganin ci gabanta, kuma ci gaban kasar zai taimaka ga tabbatar da karin ci gaban duniya.

Al’ummar kasar Sin na son hada hannu da takwarorinsu na duniya, don rungumar kyakkyawar makomar dan Adam ta bai daya. (Mai zane:Mustapha Bulama)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojoji Sun Cafke Mutum 40 Masu Yi Wa ‘Yan Ta’adda Safarar Kayan Abinci

Next Post

PDP Ta Maka Gwamnan Kwara, Abdulrazaq Kotu Kan Zargin Amfani Da Takardun Bogi 

Related

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu
Daga Birnin Sin

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

4 hours ago
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO
Daga Birnin Sin

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

5 hours ago
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles
Daga Birnin Sin

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

6 hours ago
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

7 hours ago
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

8 hours ago
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

1 day ago
Next Post
PDP Ta Maka Gwamnan Kwara, Abdulrazaq Kotu Kan Zargin Amfani Da Takardun Bogi 

PDP Ta Maka Gwamnan Kwara, Abdulrazaq Kotu Kan Zargin Amfani Da Takardun Bogi 

LABARAI MASU NASABA

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.