• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Takardun Kudin Da Suka Shaida Yadda Kasashen Duniya Suka Ci Gajiyar Ci Gaban Kasar Sin

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Takardun Kudin Da Suka Shaida Yadda Kasashen Duniya Suka Ci Gajiyar Ci Gaban Kasar Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jama’a, in kun yi la’akari da takardun kudi na kasa da kasa, za ku gano da cewa, hotunan da aka buga a takardun kudi na wasu kasashen Afirka, da ma sauran wasu kasashe masu tasowa, suna da alaka da kasar Sin.

Zanenmu na yau ya kuma nuna wasu abubuwan da aka buga a takardun kudi na kasashen Aljeriya, da Sudan, da Madagarscar da Malawi, wadanda suke da alaka da kasar Sin.

  • Tattalin Arzikin Kasar Sin Na Ci Gaba Da Farfadowa A Bana

In mun dauki takardun kudi na Aljeriya ga misali, za mu ga cewa, an buga hoton babban masallacin kasar da aka sanyawa sunan Djamaa el Djazaïr, a takardun kudin kasar mai darajar Dinar 1000, masallacin da ma’aikatan kasar Sin suka shafe tsawon shekaru shida suna ginawa, bayan daidaita wahalhalu da dama da suka fuskanta.

An kaddamar da masallacin ne a shekarar 2017, wanda ke iya daukar musulmi kimanin dubu 36 a lokaci guda, wanda kuma ya kasance babban masallaci mafi girma na farko a nahiyar Afirka, kuma na uku a duniya baki daya.

Sai kuma a takardun kudin kasar masu darajar Dinar 500, inda aka buga hoton tauraron dan Adam na sadarwa na farko a kansa, tauraron da ya kasance irinsa na farko a kasar, wanda kasar Sin ta yi nazarinsa tare da harba shi a shekarar 2017, wanda ya taimaka wajen daidaita matsalolin sadarwa da suka shafi rediyo, da talabijin da yanar gizo, da samar da ilmi da sauransu a kasar.

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Baya ga haka, a kasar Sudan, madatsar ruwa ta Upper Atbara da kamfanin kasar Sin ya dauki nauyin ginawa, ta taka muhimmiyar rawa wajen daidaita matsalolin samar da wutar lantarki, da ruwan sha, da kuma ban ruwa ga miliyoyin al’ummar kasar, wadda kuma ta samar da gudummawar bunkasa tattalin arziki da zaman rayuwar al’umma na kasar.

Sai kuma a Madagarscar, fasahar inganta irin shinkafa da masanan ilmin noma na kasar Sin suka samar ta sa yawan shinkafar da aka samar a kasar ta karu da yawan gaske, matakin da ya daidaita matsalar abinci ga al’ummar kasar da ke yawan dogara ga shinkafa. Domin bayyana godiyarsu, kasashen biyu sun buga hotunansu a takardun kudin su.

Hakika, irin wadannan labarai ba sa lisaftuwa. Cikin shekaru 10 da suka wuce, bisa ga shawarar Ziri Daya da Hanya Daya, an aiwatar da shirye-shiryen gina gadoji, da tashoshin jiragen ruwa, da hanyoyin mota, da layukan dogo, da tashoshin samar da wuta, da filayen wasa da dai sauransu da dama a kasashen Afirka da ma sauran kasashe masu tasowa, wadanda suka ba da babbar gudummawa ga bunkasuwar kasashen, da ma rayuwar al’ummominsu.

A yayin da kasar Sin ta samu gaggarumin ci gaban tattalin arziki da zaman al’umma, ta kuma yi kokarin raba nasarorinta ga sauran kasashen duniya, kasancewarta tana rungumar makomar dan Adam ta bai daya.

Kwanan nan, an bude babban taron wakilan jam’iyyar kwaminis da ke kan karagar mulki a kasar Sin ko (JKS) karo na 20, kuma a rahoton da ya gabatar wajen taron, babban sakataren kwamitin kolin jam’iyyar mista Xi Jinping ya yi nuni da cewa, kasar Sin za ta karfafa hadin gwiwa da kasashe masu tasowa bisa sahihanci da gaskiya, don kiyaye moriyarsu ta bai daya. A sa’i daya, kasar ta kuma, yi kira ga kasashen duniya da su yayata manufar kishin zaman lafiya, da ci gaba, da adalci, da dimokuradiyya da ‘yanci, don al’ummomin kasashe daban daban su kara kishin juna, su kuma martaba mabambantan wayewar kan duniya, su kara yin mu’amala da juna ta fannin al’adu, ta yadda za su kawar da sabani da rikice-rikice da suke fuskanta.

Zaman duniya, cude-ni-in-cude-ka ne. A ganin kasar Sin, da ci gaban duniya baki daya za a tabbatar da ganin ci gabanta, kuma ci gaban kasar zai taimaka ga tabbatar da karin ci gaban duniya.

Al’ummar kasar Sin na son hada hannu da takwarorinsu na duniya, don rungumar kyakkyawar makomar dan Adam ta bai daya. (Mai zane:Mustapha Bulama)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojoji Sun Cafke Mutum 40 Masu Yi Wa ‘Yan Ta’adda Safarar Kayan Abinci

Next Post

PDP Ta Maka Gwamnan Kwara, Abdulrazaq Kotu Kan Zargin Amfani Da Takardun Bogi 

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

16 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

17 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

19 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

22 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

23 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

24 hours ago
Next Post
PDP Ta Maka Gwamnan Kwara, Abdulrazaq Kotu Kan Zargin Amfani Da Takardun Bogi 

PDP Ta Maka Gwamnan Kwara, Abdulrazaq Kotu Kan Zargin Amfani Da Takardun Bogi 

LABARAI MASU NASABA

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Kasar Sin

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.