ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PDP Ta Maka Gwamnan Kwara, Abdulrazaq Kotu Kan Zargin Amfani Da Takardun Bogi 

by Sadiq
4 years ago
PDP

An gurfanar da Gwamnan Jihar Kwara, Abdulrahman Abdulrasaq a gaban wata Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, bisa zarginsa da yin amfani da takardar shaidar kammala karatu ta WAEC ta bogi wajen tsayawa takarar gwamna a zaben 2023 a Jihar.

A karar da jam’iyyar PDP ta shigar a kansa, an bukaci babbar kotun tarayya da ta haramta wa gwamna da jam’iyyar APC shiga zaben gwamna na shekara mai zuwa.

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Hakimi, Sun Yi Awon Gaba Da ‘Ya’Yansa 5 A Filato 
  • Fyade: An Yi Wa Wani Mutum Hukuncin Daurin Rai Da Rai A Ekiti

Sabuwar karar mai lamba FHC/ABJ/CS/1324/22 ta shigar da kara ne a madadin PDP ta hannun wani babban lauyan Nijeriya, SAN, Cif Paul Erokoro, tare da Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta (INEC), Abdulrahman Abdulrasaq da APC, a matsayin wanda ake tuhuma na 1 zuwa na 3.

ADVERTISEMENT

An bukaci kotun da ta yi amfani da sashe na 171 da 285 na kundin tsarin mulkin kasar nan na 1999 da kuma sashe na 29 na dokar zabe domin soke shirin da gwamnan zai yi a zabe mai zuwa.

PDP ta kuma roki kotun da ta tilasta wa INEC da ta cire gwamnan da APC daga jerin sunayen ‘yan takara da jam’iyyu da aka tantance.

LABARAI MASU NASABA

Ka Da Ku Siyar Da Gidajenku Don Sayen Hannun Jarin Matatar Dangote – Sanusi II

2027: Za Mu Kawo Wa Tinubu Kano Duk Da Tasirin Kwankwaso – Kofa

Jam’iyyar PDP ta bayyana cewa takardar shaidar kammala karatu ta WAEC da gwamna ya mika ta hannun jam’iyyar APC domin ta taimaka masa wajen neman ilimi kamar yadda sashe na 177 na kundin tsarin mulkin shekarar 1999 ya tanada ta jabu ce.

A halin da ake ciki, mai shari’a Inyang Edem Ekwo ya sanya ranar 28 ga watan Oktoba domin sauraren karar.

MASU ALAKA

Ka Da Ku Siyar Da Gidajenku Don Sayen Hannun Jarin Matatar Dangote – Sanusi II
Manyan Labarai

Ka Da Ku Siyar Da Gidajenku Don Sayen Hannun Jarin Matatar Dangote – Sanusi II

September 17, 2026
2027: Za Mu Kawo Wa Tinubu Kano Duk Da Tasirin Kwankwaso – Kofa
Manyan Labarai

2027: Za Mu Kawo Wa Tinubu Kano Duk Da Tasirin Kwankwaso – Kofa

September 17, 2026
An Ci TikTok Tarar Fam Miliyan £12.7 Kan Karya Dokar Kananan Yara A Burtaniya
Manyan Labarai

Hisbah Ta Cika Hannu Da Fitaccen Ɗan TikTok A Kano Kan Bidiyoyin Rashin Da’a

September 17, 2026
Next Post
Kasar Sin Ce Babbar Misali Na Yadda Ya Kamata Demokradiyya Ta Kasance

Kasar Sin Ce Babbar Misali Na Yadda Ya Kamata Demokradiyya Ta Kasance

LABARAI MASU NASABA

ICPC Ta Yi Wa Dan Takarar APC A Ekiti Titsiye Kan Zargin Badakalar Kuɗi

ICPC Ta Yi Wa Dan Takarar APC A Ekiti Titsiye Kan Zargin Badakalar Kuɗi

September 18, 2026
Gyaran Kundin Tsarin Mulki: Abubuwa 12 Da Ya Kamata A Sani Kan Abin Da Aka Aika Wa Majalisun Jihohi

Gyaran Kundin Tsarin Mulki: Abubuwa 12 Da Ya Kamata A Sani Kan Abin Da Aka Aika Wa Majalisun Jihohi

September 18, 2026
Saudiyya Ta Yi Biris Da Bukatar Nijeriya Ta Ƙarin Kujerun Hajjin 2027

Saudiyya Ta Yi Biris Da Bukatar Nijeriya Ta Ƙarin Kujerun Hajjin 2027

September 18, 2026
Dalilanmu Na Neman NDLEA Ta Binciki Bello El-Rufai Kan Zargin Amfani Da Hodar Iblis

Dalilanmu Na Neman NDLEA Ta Binciki Bello El-Rufai Kan Zargin Amfani Da Hodar Iblis

September 18, 2026
Shettima Ya Yi Karin Haske Kan Maganar Gwamnonin Arewa 6

Shettima Ya Yi Karin Haske Kan Maganar Gwamnonin Arewa 6

September 18, 2026
Cinikin Shige Da Fice Mai Dorewa Ba Tare Da Gurbatta Muhalli Ba Na Kasar Sin Yana Sahun Gaba A Duniya

Cinikin Shige Da Fice Mai Dorewa Ba Tare Da Gurbatta Muhalli Ba Na Kasar Sin Yana Sahun Gaba A Duniya

September 17, 2026
U-20: Nijeriya Ta Doke Ingila Da Ci 3-0, Ta Kai Zagayen Kwata-fainal

U-20: Nijeriya Ta Doke Ingila Da Ci 3-0, Ta Kai Zagayen Kwata-fainal

September 17, 2026
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Zaman Lafiya Da Tsaro Na Sin Da Afirka Karo Na Hudu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Zaman Lafiya Da Tsaro Na Sin Da Afirka Karo Na Hudu

September 17, 2026
Yadda Hadin Gwiwar BRICS Ke Ingiza Ci Gaban Kasashe Masu Tasowa

Yadda Hadin Gwiwar BRICS Ke Ingiza Ci Gaban Kasashe Masu Tasowa

September 17, 2026
Nazarin CGTN: Baje Koli Na Sin Da ASEAN Ya Nuna Kudurin Sin Na Bunkasa Bude Kofa

Nazarin CGTN: Baje Koli Na Sin Da ASEAN Ya Nuna Kudurin Sin Na Bunkasa Bude Kofa

September 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.