• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tallafa Wa Al’umma: Ya Dace Gwamnoni Su Yi Koyi Da Jihar Zamfara – UNDP

by Sulaiman
6 months ago
Zamfara

Hukumar Raya Ƙasashe ta Majalisar Ɗinkin Duniya (UNDP) ta yaba wa Gwamna Dauda Lawal bisa jajircewarsa wajen ba da tallafin da zai amfani al’ummar jihar Zamfara.

 

A ranar Laraba ne hukumar UNDP ta ƙaddamar da Cibiyar Magance Ƙalubalen Ci Gaba a Yankin Arewa maso Yamma ‘Northwest Prevention Facility Project’ a ɗakin taro na Garba Nadama da ke sakatariyar jihar, Gusau.

  • 2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara 
  • Dalilin Da Zai Iya Hana Ni Sake Bugawa Manchester United Wasa – Rashford

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa aikin ya haɗa da raba kayan noman rani ga manoma 300 da aka zabo bisa la’akari da buƙatunsu.

 

LABARAI MASU NASABA

An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

Gwamnatin Nijar Ta Yaye Tsofaffin Mayaka 369 Da Aka Bai Wa Horon Sauya Tunani

Sanarwar ta ƙara da cewa, ’yan kasuwa 1,000 za su samu jarin fara aiki na Naira 150,000 kowannensu, da nufin sauya akalar kasuwancin su zuwa sana’o’i na zamani a faɗin Jihar Zamfara.

 

A nasa jawabin, Gwamna Dauda Lawal ya jaddada cewa bayan hawansa mulki, gwamnatinsa ta bullo da shirye-shiryen ƙarfafawa da dama tare da samar da damarmaki don cimma manufofinsa na ceto.

 

“Waɗannan tsare-tsare ba wani kebantaccen abu ba ne, wani ɓangare ne na babban burinmu wajen samar da jihar Zamfara mai albarka don haɗa abokan hulɗa don magance ɗimbim matsalolin zamantakewa da tattalin arziki.

Zamfara

“Yawancin tsare-tsare na rage raɗaɗin talauci da wannan gwamnati ta bullo da su sun yi tasiri ga rayuwar dubban ‘yan jihar, ƙudirin gwamnatinmu na kawar da raɗaɗin talauci yana haifar da ɗa mai ido. Za mu ci gaba da yin haɗin gwiwa tare da UNDP da sauran ƙungiyoyin masu ba da tallafi don samar da ɗorewar hanyoyi don fitar da mutanenmu daga ƙangin talauci.

 

“Tun da aka fara wannan shirin na bayyana cewa akwai tsari wajen zabi na gaskiya na waɗanda za su ci gajiyar shirin, don haka an zabo waɗanda suka amfana daga garuruwa da ƙauyuka kamar Sankalawa, Furfuri, Karal, Gusau, da Bungudu.

 

“Ina yawan nanata cewa ƙarfafa tattalin arziki dole ne ya kasance cikin haɗin kai a ƙarƙashin mu, ba tare da barin al’umma a baya ba, shi ya sa na dage wajen ganin an rarraba damarmaki cikin adalci a dukkan ƙananan hukumomin.

 

“Hakazalika, an gudanar da shirye-shiryen horarwa ga duk waɗanda suka ci gajiyar noman rani. Mun yi imani da cewa samar da albarkatu ba tare da ilimin yadda za a yi amfani da su ba, zai iya iyakance tasirin da shirin ke son cimma.”

 

Gwamna Lawal ya kuma miƙa godiyarsa ga Hukumar Raya Ƙasashe ta Majalisar Ɗinkin Duniya kan yadda suka amince da manufofin gwamnatinsa na ci gaba. “Ga waɗanda suka ci gajiyar, ina ba ku umarni da ku yi amfani da waɗannan albarkatun bisa ga gaskiya, kar ku ba ni kunya a kan yardar da nake da ita akan ku.

Zamfara

“Da waɗannan kalamai, abin farin ciki ne na a hukumance na ƙaddamar da rabon kayayyakin noman rani ga masu cin gajiyar 300 tare da raba jarin fara aikin na N150,000.00 ga ‘yan kasuwa 1,000.”

 

Tun da farko, shugaban ofishin UNDP na Arewa maso Yammacin Nijeriya, Ashraf Usman, ya bayyana cewa tasiri, sha’awa, da azamar gwamnatin jihar Zamfara a bayyane yake ga kowa da kowa, wanda ke da matuƙar muhimmanci ga haɗin gwiwar.

 

“Na gode Mai girma Gwamna, waɗannan su ne dalilan da suka sa muka zo nan, ina taya ku murna da goyon bayan ɗimbin jama’a, na gode da irin misalin da ka ke bai wa sauran gwamnatocin jihohi wajen samar wa al’umma tallafi. Na gode da irin jagorancin ka.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza
Labarai

An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

October 19, 2025
Nijar
Labarai

Gwamnatin Nijar Ta Yaye Tsofaffin Mayaka 369 Da Aka Bai Wa Horon Sauya Tunani

October 19, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus
Manyan Labarai

‘Yan Siyasa 11 Da Suka Faɗa Dambarwar Takardar Shaidar Karatu Ta Bogi

October 19, 2025
Next Post
Gwamnati Za Ta Kwace Gidajen Ma’aikatan Da Suka Yi Ritaya Ba Su Biya Bashin Gidaje Ba

Gwamnati Za Ta Kwace Gidajen Ma'aikatan Da Suka Yi Ritaya Ba Su Biya Bashin Gidaje Ba

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ake Alkaki

Yadda Ake Alkaki

October 19, 2025
Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (1)

Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (2)

October 19, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

October 19, 2025
Nijar

Gwamnatin Nijar Ta Yaye Tsofaffin Mayaka 369 Da Aka Bai Wa Horon Sauya Tunani

October 19, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

‘Yan Siyasa 11 Da Suka Faɗa Dambarwar Takardar Shaidar Karatu Ta Bogi

October 19, 2025
gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.