• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tallafin Da Amurka Ta Baiwa Gaza Wasan Kwaikwayo Ne

by CGTN Hausa
2 years ago
in Ra'ayi Riga
0
Tallafin Da Amurka Ta Baiwa Gaza Wasan Kwaikwayo Ne
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanan baya, Isra’ila ta ci gaba da kaiwa zirin Gaza hare-hare, lamarin da ya yi sanadin asarar rayuka da dama. Amurka ce ta samar da da yawa daga cikin makaman da Isra’ila ta yi amfani da su. Bisa labarin da shafin yanar gizo na jaridar kasar Isra’ila wato Ha’aretz ya bayar, an ce, Amurka ta shafe tsawon watanni 5 tana jigilar makamai ta sama zuwa Isra’ila.

A wani bangare Amurka na tallafawa Isra’ila da makamai, yayin da a wani bangare na daban kuwa, ta yanke shawarar jefa wa fararen hula a Gaza abinci daga sama. Sai dai daga cikin dubban abincin da ta jefa, yawancinsu sun fada ne cikin teku, wadanda suka kasa biyan bukatun fararen hular Gaza da yawansu ya haura miliyan 2. Ban da wannan kuma, sakamakon yadda laimar sauka daga jirgin sama masu dauke da abincin sun gaza budewa cikin lokaci, ya sa abincin ya fada kai tsaye kan wasu gidaje da mutane dake kasa, abin da ya sa mutane 5 suka mutu.

  • Mun Gano Famfo 5,570 Da Ake Amfani Da Su Wajen Satar Danyen Mai — NNPCL
  • Jamhuriyar Congo Tana Son Karfafa Zumunta Da Hadin Gwiwa Da Sin

Shin ko da gaske ne Amurka tana mai da hankali kan rikicin jin kai dake faruwa a Gaza?

Kungiyoyin jin kai da dama sun yi tir da hanyar da Amurka ta zaba ta samar da tallafin jin kai ta hanyar jefa abinci daga sama. A ganinsu, a maimakon bukatar kawarta wato Isra’ila da ta bude hanyoyin jin kai, ko daina samarwa Isra’ila makamai, Amurka ta zabi hanyar da ba ta dace ba, wato jefa abinci daga sama, kuma burin da take neman cimmawa shi ne samun goyon baya daga masu kada kuri’u a gida.

Ban da wannan kuma, shugaban kasar Amurka Joseph Biden ya sanar da shirin kafa wata tashar jirgin ruwa ta wucin gadi a gabar tekun bahar Rum dake Gaza, don baiwa yankin tallafin jin kai. Hakan ya jawo suka daga masu bibbiyar kafar sada zumunta ta X, wadanda suka yi zargin cewa, Amurka tana da karfin dakatar da rikicin da ake fuskanta a Gaza muddin ta daina samarwa Isra’ila makamai, amma ta yi wasan kwaikwayo na samar da tallafin jin kai.

Labarai Masu Nasaba

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

Tallafin da Amurka ta bayar da kyar sun isa hannun fararen hula, amma makaman da ta samar sun halaka mutane masu dimbin yawa. ‘Yan siyasar Amurka su kan yi wasan kwaikwayo don samun kuri’u, amma a wannan karo masu gudun hijira ke yin asara, wadanda ba su da abinci ba su da gidaje kuma ba su da tsaro, ballantana hakkin Bil Adama. Shin ko ‘yan siyasar Amurka ba su jin kunya? (Mai zana da rubutu: MINA)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaGazaTallafi
ShareTweetSendShare
Previous Post

SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 4

Next Post

Irin Babban Taron LEADERSHIP ‘Yan Nijeriya Ke Bukata

Related

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

3 hours ago
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
Ra'ayi Riga

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

2 days ago
Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba
Ra'ayi Riga

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

1 week ago
Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

2 weeks ago
Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa
Ra'ayi Riga

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

2 weeks ago
Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 
Ra'ayi Riga

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

2 weeks ago
Next Post
Irin Babban Taron LEADERSHIP ‘Yan Nijeriya Ke Bukata

Irin Babban Taron LEADERSHIP ‘Yan Nijeriya Ke Bukata

LABARAI MASU NASABA

NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

September 18, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

September 18, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

September 18, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.